27.5 C
Abuja
Wednesday, March 22, 2023

Allahu Akbar: Bidiyon jakin da wata mata ta haifa a garin Zaria

LabaraiAllahu Akbar: Bidiyon jakin da wata mata ta haifa a garin Zaria

A duk lokacin da aka kira Allah, Ubangiji mahalicci, dole mutum ya yarda da cewa shi ne mai yin komai da kuma kowa.

A ranar Talata, 21 ga watan Maris na shekarar 2022 da yamma labarin yadda wata mata ta haifi wata halitta mai kama da doki ya bazu a garin Zaria cikin Jihar Kaduna.

Lamarin ya faru ne a layin Lemu da ke Tudun wadan Zaria kamar yadda ganau suka shaida wa wakilin Labarun Hausa.

Bayan isa gidan da lamarin mai ban al’ajabi ya faru, wakilin Labarun Hausa bai samu damar ganawa da matar da ta haifi jaririn dokin ba, amma ya gan ta kuma makwabtan ta sun tabbatar masa da hakan.

Anan ne ma wakilin namu ya samu bidiyon halittar mai kama da doki wanda tuni ya fara bazuwa a shafukan sada zumunta.

Mutanen gidan sun bayyana yadda aka birne halittar kasancewar abu ne mai ban tsoro da kuma mamaki ace dan adam ya haifi dabba.

Ku ci gaba da kasancewa tare da mu, nan ba da jimawa ba, zamu kawo muku cikakken bayani akan yadda wannan lamari mai firgitarwa ya faru.

‘Yan sanda sun cafke wata mata wacce ta ƙona ɗuwawun ɗiyar mijinta da wuƙa mai zafi

‘Yan sandan jihar Bayelsa sun cafke wata mata mai suna Esther Otoniye, bisa laifin ƙona ɗuwawun ɗiyar mijin ta mai shekaru 10 da wuƙa mai zafi.

Otinoye wacce aka cafke a gidan su da ke Akenfa wajen birnin Yenagoa, babban birnin jihar, ta bayyana cewa ƙaramar yarinyar ta sharara mata ƙarya ne. Jaridar Independent.ng ta rahoto.

Jikin ƙaramar yarinyar yasha tabbai sosai waɗanda aka zargin ta same su ne ta hanyar shan bugu sosai.

‘Yan sanda sun ɗamƙe matar

An samo cewa a ranar Asabar, kwamishinan ‘yan sandan jihar Ben Okolo, ya bayar da umurnin cafke Otinoye bayan wasu ƙungiyoyin kare haƙƙin mata da ƙananun yara sun shigar da ƙorafe-ƙorafe a kan ta.

Sai dai ta musanta ƙona ɗuwawun yarinyar da wuƙa mai zafi, inda ta bayyana cewa ruwan zafi ne ya zubo mata a ɗuwawun bisa tsautsayi.

Amma, yarinyar ta amsa cewa ta sharara wa matar ƙarya inda ta hukunta ta hanyar ƙona mata ɗuwawu da wuƙa mai zafi.

Ɓangaren kula da jinsi na hukumar ‘yan sandan jihar ma su lura da lamarin sun miƙa yarinyar asibitin ‘yan sanda domin duba lafiyar ta.

Hukumomi sun tabbatar da aukuwar lamarin

Kakakin ‘yan sandan jihar, SP Asinim Butswat, ya tabbatar da cafke Esther Otinoye bisa tuhumar aikata laifin, inda ya bayyana cewa an miƙa lamarin zuwa ga hannun ‘State Criminal Investigation and Intelligence Department’ (SCIID).

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

WhatsApp Group

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: hello@labarunhausa.com

Ku duba wasu labaran mu

Check out other tags:

Labaran da suka fi tashe