LabaraiMai garkuwa da mutane ya fusata ya fasa kwai...

Mai garkuwa da mutane ya fusata ya fasa kwai bayan ya raina kason da aka bashi

-

- Advertisment -spot_img

Wani mai garkuwa da mutane da ya shiga hannun hukuma ya bayyana yadda ya tona asirin abokan harƙallar sa bayan sun biya shi naira dubu ɗari biyu (N200,000) kacal daga cikin naira miliyan 12 da su ka amsa a matsayin kuɗin fansar wasu mutum biyu.

Mutumin mai suna Sadu Bunkawu, wanda bai gamsu da kason da aka bashi ba, ya garzaya zuwa ofishin ‘yan sanda inda ya bayyana laifukan sa. Pulse.ng ta rahoto

Garkuwa da mutane
Mai garkuwa da mutane ya fasa kwai bayan ya raina kason da aka bashi. Hoto daga Pulse.ng

Ya bayyana yadda lamarin ya auku

Bunkawu mai shekaru 28, ɗan asalin ƙauyen Filingo ne a ƙaramar hukumar Jada ta jihar Adamawa. Ya bayyana cewa an biya abokan harƙallar sa naira miliyan 12 na kuɗun fansar wasu mutum biyu Umaru Diffawa da Umaru Babidi mazauna ƙauyen.

Rashin gamsuwa da yadda aka kasafta kuɗin, ya sanya ya garzaya zuwa wajen ‘yan sanda domin su kwato masa hakkin sa.

Bunkawu ya ciza yatsa kan rashin sa’ar sa a cikin aikin inda dubu ɗari biyun da ya ƙarba ta faɗi akan hanyar sa komawa gida.

Na rasa kason da na samu a kuɗin yayin da na ke saurin komawa gida akan lokaci

Mu bakwai iyalan waɗanda aka ɗauke ɗin su ka ba kuɗin. Bayan mun sake su an kirani inda aka bani N200,000 kacal

A cewar sa

An maka shi gaban kotu

Sai dai ‘yan sanda sun maka shi gaban kotun majistare ta ɗaya a Yola bisa laifin ƙitsa laifi da yin garkuwa da mutane.

Bunkawu ya amsa dukkanin tuhumomin da ake masa inda alƙalin kotun Muhammad Abdullahi ya ɗaga shari’ar zuwa 4 ga watan Afrilun 2022.

Ku dauki makamai domin kare kanku daga ‘yan bindiga, jami’an tsaro sun gaza -gwamna ga ‘yan jihar sa

Gwamnan jihar Benue, Samuel Ortom ya buƙaci mazaunan jihar sa musamman waɗanda ke zama a ƙauyuka da su ɗauki halastattun makamai domin kare kawu nan su daga ‘yan ta’adda.

Ya bayyana cewa hakan ya zama wajibi ne  saboda yanzu an wuce da yayin cigaba da kiran neman ɗauki. Jaridar Daily Trust ta rahoto

Dole ne mu kasance cikin shirin ko ta kwana wajen tunkarar ‘yan ta’adda. Wannan wata hanya ce da zamu iya taimakawa jami’an tsaro wajen daƙile wannan matsalar tunda abubuwa sun yi musu yawa.

A cewar sa

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

WhatsApp Group

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: hello@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you