LabaraiGurguwar budurwa mai shekaru 70 ta ce saurayi danye...

Gurguwar budurwa mai shekaru 70 ta ce saurayi danye shakaf mai shekaru 21 take so ta aura

-

- Advertisment -spot_img
  • Wata budurwa yar shekara 70, mai suna Genevieve ta bayyana muradin ta na auren saurayi mai shekaru 21
  • Matar, wacce bata taba barin gidan ta ba, ta bayyana yadda bata taba saurayi ba, kuma batasan dadin soyayya ba
  • Genevieve ta dau tsawon shekaru tana rayuwa cikin yanayi mara dadi, saboda matsalar lafiyar kafa da take fama dashi

Wata budurwa ‘yar shekara 70, mai suna Genevieve, wacce bata taba kusantar wani ba, duk ba ita ta zabi hakan ba; sai dai a cewarta haka rayuwa tayi da ita, Legit.ng ta ruwaito.
Genevieve tana fama da matsalar gurgunta, hakan ya tilasta mata rarrafe saboda bazata iya amfani da kafar ta ba; bata taba tafiya ba a rayuwarta.
Kuma bata taba saurayi ba ko samun ilimi ingantacce.

Gurguwar budurwa mai shekaru 70 ta ce saurayi danye shakaf mai shekaru 21 take so ta aura
Gurguwar budurwa mai shekaru 70 ta ce saurayi danye shakaf mai shekaru 21 take so ta aura

Yayin zantawa da Afrimax, gurguwar budurwa ta ce, an haifeta a shekarar 1952.
Sai dai, a lokacin da iyayen ta suka farga diyar tasu bata iya tafiya, cigaba da rarrafe tayi. Sun yi zaton lamarin zai canza idan ta kara tasawa, amma hakan bai kasance ba.

Budurwar ta bayyana yadda tayi fama da cuta a lokacin da tana yarinya, wanda hakan ne ya shafi kafarta, kuma yasa ta zama lalura ga iyayenta.

Iyayen Genevieve basu tura ta makaranta ba, saboda basu da kudin siya ma ta kujerar guragu, sannan ba za su iya kai ta da dawo da ita kullum ba.

Baya ga rashin samun damar neman ilimi, halin da take ciki ya hana ta samun masoyi.

Saurayi ya halaka budurwarsa, ya kira ‘yan uwanta ya sanar musu sannan ya cika wandonsa da isa

Ana zargin wani saurayi da kashe budurwarsa a Abuja, ya kuma sanar da ‘yan uwanta cewa “su zo su dauki gawar ta”.

A watan Mayun 2021, kuma ya shiga cikin watan Agusta na wannan shekarar, an bayyana cewa wanda ake zargin ya koma gidan marigayiyar ne saboda ba shi da aikin yi kuma ba shi da wurin kwana.

An ruwaito cewa Evelyn ta sauke nauyin kudi na Ugochukwu, wanda aka ce ya yi mata fyade ko kadan.

Ta yi shirin ficewa daga falon saboda cin zarafinta da yake yi. Sai dai kuma a ranar Asabar, 19 ga watan Fabreru, sun samu saɓani inda ya shaƙe ta har lahira ya gudu.

“Bayan ya gudu zuwa wani wurin ɓuya, Ugochukwu ya kira mahaifin Evelyn a kauyen yana tsoratar da shi game da mutuwar Evelyn, cewa ya zo ya ɗauki gawar ‘yarsa.

“Ya kuma kira wani surikin sa ya ce masa haka. Uban ne ya kira daga ƙauye ya sanar da ‘yan uwa a Abuja. Haka labarin ya kasance.” Wata majiya ta ce.


Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan sanda sun gano gawar ta a ranar Litinin, 21 ga watan Fabrairu.

Abokan marigayiyar sun yi ta yadawa a shafukan sada zumunta na yanar gizo suna jimamin rasuwar ta.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayinku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausaagmail-com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you