LabaraiYadda Amarya ta rasa ran ta ana tsaka da...

Yadda Amarya ta rasa ran ta ana tsaka da daurin auren ta

-

- Advertisment -spot_img

Wata amarya mai suna Bilkisu Umar Tantoli ta rasu ranar Juma’a 25 ga watan Fabrairun 2022, Muryar ‘Yanci ta ruwaito.

Limamin babban masallacin Juma’a na Nasarawa da ke garin Kaduna, Liman Jabiru Isah Na’ibi ya bukaci dangin amarya da ango su shigo a daura aka sanar da shi cewa Allah ya dauki ran amaryar.

amarsu
Yadda Amarya ta rasa ran ta ana tsaka da daurin auren ta

Take anan ango ya shiga mummunan yana yi inda aka zarce da shi gida bayan samun labarin rasuwar amaryar.

Muna fatan Ubangiji ya gafarta mata ya kuma sada ta da mala’ikun rahama, ameen.

Daga Sani Yusuf Nasarawa, kamar yadda shafin Muryar ‘Yanci na Facebook ya ruwaito.

Miyagun ‘yan bindiga sun yi garkuwa da amarya da wasu mutum 5 a Kaduna

Wasu miyagun ‘yan bindiga sun kai farmaki kauyen Rigachikun da ke ƙaramar hukumar Igabi a jihar Kaduna inda suka yi awon gaba da wata amarya da aka kusa auren ta da wasu mutane biyar.

An rawaito cewa ‘yan bindigar sun afkawa al’ummar da ke kusa da madatsar ruwan kasan da misalin ƙarfe ɗaya na safiyar ranar Laraba, 23 ga watan Fabrairu, inda suka far wa gidaje uku tare da tasa ƙeyar waɗanda abin ya shafa zuwa inda ba a sani ba.

Wata mata da jikokinta na cikin waɗanda aka sace tare da amaryar da aka bayyana sunanta da Khadija. Tana kwance a gefenta lokacin da ‘yan bindigan suka shiga ɗakin su.

“Muna cikin bacci suka shigo daki suka ce Khadija da Shabilu su taho tare da su, kuma suka kwashe waya da biredi a teburin, duk muka rude.” Ta shaida wa Aminiya.


Wani shugaban al’ummar yankin, Idris Abdulrasheed, ya ce lamarin shi ne na farko a cikin al’ummar kuma tuni suka sanar da ‘yan sanda lamarin.

Ya ce har yanzu ‘yan fashin ba su tuntubi iyalan wadanda abin ya shafa ba.

A halin da ake ciki, wani Comr Jameel Abdulkarim, ya bayyana ɗaya daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da shi a matsayin Muktar Abdulsalam.

Muktar a cewarsa, shi ne mataimakin Shugaban Hukumar SUBEB a Kaduna.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausaagmail-com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you