LabaraiWani magidanci ya cinnawa matarsa wuta, ƴan sanda sun...

Wani magidanci ya cinnawa matarsa wuta, ƴan sanda sun bazama nemansa

-

- Advertisment -spot_img

Hukumar ƴan sandan jihar Legas ta bazama neman wani magidanci ruwa a jallo bayan ya cinnawa matarsa wuta.

Magidancin mai suna Akpos ana zarginsa da cinnawa matarsa mai suna Risikat, wuta wacce tayi sanadiyyar rasuwarta a mazaunin su dake kan titin  Ayide Osolo, Divine Estate, a yankin Ijanikin na jihar Legas. Shafin LIB ya rahoto.

Lamarin ya auku ne a gidan ma’auratan

Shaidun gani da cewa sun tabbatar cewa Akpos da Risikat suna tare a cikin gidansu lokacin da rigima ta ɓarke a tsakanin su.

Rigimar tayi ta ruruwa wanda har ya kai ga Akpos ya ɗauko jarkar man fetur ɗin su ya ƙwararawa matar sa sannan ya banka mata wuta.

Bayan ya fahimci girman aika-aikar da ya tafka, sai magidancin ya ranta a na kare wanda har yanzu ba a san inda yake ba

Makwabta sun garzaya da Risikat zuwa wani asibiti mafi kusa da su inda daga bisani ta rasu yayin da ake duba lafiyarta bisa ƙunannakin data samu.

Ƴan sanda na neman magidancin ruwa a jallo

Da yake tabbatar da aukuwar lamarin, kakakin hukumar ƴan sandan, SP Benjamin Hundeyin, ya bayyana cewa:

“An shigar da wani ƙorafi a ofishin ƴan sanda na Ijanikin cewa wata mata mai suna Risikat, mai shekara 48 a duniya, sun yi rigima da mijinta wanda suna cikin rigimar ya ƙwarara mata man fetur sannan ya cinna mata wuta.”

“Lamarin ya sanya ta samu munanan raunikan ƙuna sannan an garzaya da ita zuwa asibiti domin duba lafiyarta amma ta rasu. Ana ƙoƙarin ganin an cafko wanda ake zargin tun bayan tserewar sa.”

Magidanci ya cinnawa ƴaƴan matarsa wuta bayan ta ƙi yarda su yi kwanciyar aure

Wani magidanci ya cinnawa ƴaƴan matar sa guda biyar wuta bayan ta hana shi su yi kwanciyar aure.

Magidancin mai suna Ojo Joseph mai shekara 54 a duniya ya aikata wannan aika-aikar ne a jihar Ondo.

Lamarin ya auku ne a unguwar Fagun cikin garin Ondo a ranar Lahadi 6 ga watan Oktoɓan 2022 da safe.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you