LabaraiAngo ya mutu bayan kwana 2 da daurin auren...

Ango ya mutu bayan kwana 2 da daurin auren shi

-

- Advertisment -spot_img

Wani ango da aka bayyana sunan shi da alhaji Kabiru Mai Magani Saminaka ya mutu bayan kwanaki biyu da ɗaura auren sa akan hanyar sa ta dawowa Saminaka.

Angon ya mutu sakamakon haɗarin mota

Angon ya mutu ne a sakamakon mummunan haɗarin mota da faru dashi a yayin da yake komawa gida Saminaka, ƙaramar hukumar Lere jihar Kaduna daga Pambeguwa, a jihar ta Kaduna, a ranar Litinin ɗin da ta gabata.

Labarin mutuwar wannan sabon ango dai ya yaɗu cikin ƙanƙanin lokaci a kafafen sada zumunta na zamani musamman ma dai a kafar Facebook inda ‘yan uwa da abokan arziƙin mamacin suka dinga rubuta alhinin su da kuma addu’o’i.

Yaje ta’aziyyar mutuwa ne shima

Ance shima yaje wata gaisuwa ce ta mutuwa da aka yi a garin Pambeguwa dake jihar ta Kaduna a yayin da wannan haɗarin ya same shi kan hanyar komawa.

Wani mai suna Jamilu Suleiman Saminaka ya wallafa labarin mutuwar a shafin shi na Facebook inda ya bayyana cewa kwana biyu kenan da ƙara auren Alhaji Kabiru Saminaka. Ya bayyana cewa ya mutu ne akan hanyar sa ta dawowa daga wajen wata ta’aziyya da yaje Pambeguwa.

Kwanan shi biyu kenan da ƙara aure

“Innalillai wa’inna ilaihi raji’un. Bayan kwana biyu da karin Aurenshi Allah ya karbi rayuwarsa a hanyarsa tazuwa ta’aziya Garin Pambegua.

Allah yajikan Alh Kabiru bilhakki
Mai magani, ya karbi shahadarsa Alfarman Manzon Allah S. A. W. Mukuma idan tamu tazo Allah yasa mucika da Imani ” inji Jamilu Sulaiman.

Mutane da dama sunyi tsokaci na jimami gami da addu’o’i dangane da mutuwar wannan ango a hatsarin mota. Sun wallafa hotunan shagulgulan bikin wanda ba’a daɗe da yin shi ba.

FB IMG 1667964392730
FB IMG 1667964388961

Wani ma mai suna Abdullahi Usman Saminaka ya wallafa labarin gami da wallafa wani hoto na daga hotunan shagalin bikin, tare da yima mamacin addu’a.

“Inna-Lillahi-wa-Inna-Ilaihirraji’un
Allah yayima Alhaji Kabiru mai magani Rasuwa. Allah yaji kanshi yasa ya huta ameen.”

“Innalillai wa’inna ilaihi raji’un. Bayan kwana biyu da karin Aurenshi Allah ya karbi rayuwarsa a hanyarsa tazuwa ta’aziya Garin Pambegua.

Allah yajikan Alh Kabiru Mai magani, ya karbi shahadarsa Alfarman Manzon Allah S. A. W. Mukuma idan tamu tazo Allah yasa mucika da Imani.” inji wani Haruna Nuhu Saminaka.

A wani labarin na daban kuma, kunji cewa Shugaban hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa wato EFCC, Abdulrashid Bawa, yayi magana kan hukuncin kotu na tura shi zuwa gidan gyaran hali.

Wata babbar kotu a birnin tarayya Abuja mai zamanta a Maitama ta yankewa Abdulrashid Bawa hukunci bisa raina kotu.

Kotun ta umurci hukumar EFCC da ta mayarwa wani tsohon darekta a hukumar sojin sama, Air Vice Marshal (AVM) Rufus Adeniyi Ojuawo, motar sa ƙirar Range Rover, da Naira miliyan 40 (N40m).

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da saƙo ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you