LabaraiUbangiji ba ya son kyautar rainin wayau, Fasto ya...

Ubangiji ba ya son kyautar rainin wayau, Fasto ya raina N30 da aka ba shi sadaka

-

- Advertisment -spot_img

Wani fasto ya isa daidai tashar motoci inda ya dinga yi wa matafiyi wa’azi mai ratsa jiki akan muhimmancin bayar da sadaka, LIB ta ruwaito.

Anan ne wani fasinja ya dauki N30 ya ba shi, wanda ran faston yayi matukar baci. Yayin da ya ki amsar kudin, ya zargi fasinjan da raina Ubangiji inda yayi masa wankin babban bargo.

Ya tambayi fasinjan dalilin da yasa bai yi amfani da N30 din wurin siyan na’urar salula ba.

Ya kara da cewa shi ba ya kin amsar sadaka, amma Ubangiji ya tsani sadakar rainin wayau.

Lamarin ya bai wa mutane da mamaki kasancewa kowa ya san cewa sadaka ba ta kadan kuma ba ta yawa. \

Sai dai a wurin wannan faston, ya bukaci mutumin ya bayar da kudi mai kauri in har yana so ya samu cikakken lada.

Ga bidiyon:

Yadda wani babban fasto yayi wa wata matar aure fyade yayin yi mata addu’ar tsarkakewa

Wani babban fasto a wata coci a Rumuaholu a karamar hukumar Obio/Akpor, ta jihar Ribas, yayi wa wata matar aure fyade yayin yi mata addu’ar samun tsarkaka.

Wani mamba na wata kungiyar masu rajin kare hakkin bil’adama ta ‘Center for Basic Rights and Accountability Campaign’, Prince Wiro, shine ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin 10 ga watan Oktoban 2022. Jaridar Legit.ng ta rahoto.

Yadda faston yayi wa matar auren fyade

Wiro ya bayyana cewa faston yayi wa matar ta karfi bayan ya nemi mahaifiyarta da ta dan basu waje lokacin da ake addu’ar, sannan an tsare shi a ofishin ‘yan sanda na Ozuoba.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you