LabaraiBa zamu biya malaman ASUU kudin aikin da ba...

Ba zamu biya malaman ASUU kudin aikin da ba su yi ba – FG

-

- Advertisment -spot_img

Gwamnatin tarayya ta maida martani kan ƙorafe-ƙorafen da malaman jami’a na ƙungiyar ASUU da kuma sauran al’umma suke yi dangane da batun rabin albashi da aka biya su na watan Oktoban da ya gabata.

Labaran da ake yaɗawa ba gaskiya bane

Wannan martani dai na zuwa ne daga ofishin ma’aikatar kula da ayyuka ta ƙasa biyo bayan labaran da ke yawo a kafafen sadarwa dangane da rabin albashin da aka biya malaman jami’o’i na ASUU na watan da ya gabata.

Ma’aikatar tace batun biyan rabin albashi da ‘yan ASUU suke ƙorafi akai ba gaskiya bane, iyaka dai an biya su kuɗaɗen kwanakin da suka yi aiki ne, kuma lissafa aka yi, kamar yadda Vanguard ta wallafa.

Albashin da aka biyan ‘yan ASUU a lissafe yake

A tattaunawar shi da ‘yan jarida, mai magana da yawun ma’aikatar, Olajide Oshundun, ya bayyana cewa labaran da ake ta yaɗawa ba gaskiya bane, kawai dai mutane suna yaɗa labaran da basu inganta ba.

Yace albashin da aka biya ‘yan ƙungiyar ta ASUU abu ne wanda aka yi shi a lissafe. Kuma anyi hakan ne saboda baza a iya biyan su kuɗin aikin da basu yi ba.

Bamu ce a biya su rabin albashi ba.

A cikin jawabin nashi, ya bayyana cewa ministan ayyuka na ƙasa wato Chris Ngige bai bawa ma’aikatar kuɗi umarnin biyan malaman jami’o’i na ASUU rabin albashi ba.

Jawabin ya kuma ƙara da cewar biyo bayan hukunci da kotu ta yanke, inda ta umarci ƙungiyar ASUU da ta janye yajin aiki da take yi, wanda kuma tura wakilan mu domin su tabbatar cewa malaman sun koma bakin aikin su.

“Ma’aikatar mu ta tura ma ma’aikatar kuɗi da tsare-tsare ta ƙasa saƙon cewa a biya malaman na jami’a albashin su. An lissafa daga randa suka koma aiki a Oktoba, wanda dashi ne aka ƙididdige aka  biya su albashin su. Ba yadda za’a biya su kuɗin aikin da basu yi ba, kowa fa a takure yake.” inji Olajide.

Hakanan ma’aikatar kula da ayyukan ta yi martani ga shugaban ASUU na jami’ar Ɗanfodio dake Sokoto, Muhammad N. Al-Mustapha wanda ya zargi ministan da sanya son rai wajen nuna bambanci a wajen biyan wasu daga cikin ma’aikatan.

Ma’aikatar ta buƙaci al’umma da suyi watsi da duk wasu labarai da ake yaɗawa da ke nuni da cewa an nuna bambanci wajen biyan wasu daga cikin ma’aikatan.

A wani labarin na daban kuma, wata mata tace ba wani abu bane don mace ta ƙi yin aure.

Wata shahararriyar marubuciya mai suna Chimamanda Ngozi-Adichie, tace ita bata ga wani aibu ba, kan don mace taƙi yin aure ta zaɓi ta zauna ita kaɗai.

Tayi wannan kalamin ne a yayin da take gabatar da wata ƙasida a wajen wani taro a Legas wanda aka shirya kan rawar da mata ke takawa a ɓangarorin gudanarwa, kasuwanci da kuma sauran ayyukan al’umma.

Tace lokaci yayi da ya kamata mutane su daina takura ma mata akan batun ƙin yin auren su, inda tace suna da haƙƙin more yancin su yadda suke so.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you