LabaraiKaduna: Dakarun sojoji sun lalata sansanin ƴan bindiga 100,...

Kaduna: Dakarun sojoji sun lalata sansanin ƴan bindiga 100, sun tura da dama barzahu

-

- Advertisment -spot_img

Dakarun sojojin Najeriya sun halaka ƴan bindiga 152 sannan sun lalata sama da sansanin su guda 100 a jihar Kaduna.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar, Samuel Aruwan, shine ya bayyana hakan inda yace sojojin sun samu wannan nasarar ne a tsakiya da ƙarshen shekarar 2022.

Ya dai bayyana hakan ne a yayin da yake bayar da rahoton yanayin tsaro na tsakiya da ƙarshen shekarar 2022 ga gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai a ranar Juma’ah. Jaridar Vanguard ta rahoto.

An samu gagarumar nasara

“Za ka ga cewa an samu cigaba sosai tun lokacin da sojoji suka ƙara ƙaimi wurin murƙushe ƴan ta’adda a jihar a cikin watanni shida da aka haɗa rahoton.”

 “Ƴan ta’adda 152 da ƴan bindiga sojoji suka halaka a jihar, da dama an murƙushe su ne a sansanunuwan su da wajen haɗuwar su.”

“An halaka ƴan bindiga 16 a yankunan ƙananan hukumomin Birnin Gwari da Chikun, yayin da sama da sansanunuwa 100 da ƴan bindiga suke ciki aka lalata su.”

“Sojojin kuma sun ceto mutum 74 da aka yi garkuwa da su.”

Ayyukan ta’addanci sun ragu sosai a jihar

“Kashe-kashe masu alaƙa da ta’addanci da faɗace-faɗace a jihar Kaduna sun ragu matuƙa a ƙarshen shekarar nan. Haka ma an samu raguwar satar mutane da shanaye.”

“Haɗin guiwar da ake yi na haifar da ɗa mai ido. Muna godiya matuƙa ga kwamandoji, da jami’an tsaron da suke aiki ba dare ba rana domin ganin abubuwa sun daidaita. Za mu cigaba da iyaƙar bakin ƙoƙarin mu domin har yanzu akwai sauran aiki.” Inji shi

Sojoji sun halaka ‘yan ta’addan Boko Haram da dama a jihar Borno

Dakarun sojojin Najeriya sun halaka ‘yan ta’addan Boko Haram da dama a wani bata kashi da suka yi a yankin Banki na karamar hukumar Bama ta jihar Borno.

Jaridar The Cable ta rahoto cewa sojojin wadanda suka fito daga bataliya ta 151 tare da hadin guiwar ‘yan sakai (CJTF) sun afkawa maboyar ‘yan ta’addan a kauyen Gauri a ranar 30 ga watan Oktoba

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you