LabaraiWani mutum ya maka banki a kotu saboda sun...

Wani mutum ya maka banki a kotu saboda sun fallasa wa wani kuɗin asusunsa bayan ya talauce

-

- Advertisment -spot_img

An maka bankin Absa da ke Kenya gaban kotu bayan wani dan kasuwa ya zarge su da bayyana wa wani rashin kudinsa ba tare da saninsa ba, LIB ta ruwaito.

Kirui Kamwibua, mai kamfanin New Mega Africa Ltd yana neman Ksh miliyan 192 a matsayin diyyar asarar da kuma Ksh biliyan 1.2 na rasa kimar da yayi tare da Ksh miliyan 92 ta asarar kadarar da yayi bayan maka wani banki gaban kotu.

Ya bayyana cewa sun nuna wa ma’aikatansa halin talaucin da ya shiga wanda hakan ya janyo illa ga kasuwancinsa.

A cewar Kamwibua, bayan an gabatar musu da bayani dangane da matsin da ya shiga, an kawo cikas ga kasuwancinsa.

Ya ce hakan nuna cewa ma’aikacin bankin da ya bayyana sirrin asusunsa alama ce ta gazawar bankin daga adana sirrin masu ajiya a wurinsu. Kuma hakan keta hakkinsa na sirri ne.

Ya kara da cewa duk da yadda ya dinga neman bankin ta ba shi bashi inda ya dinga kai koma ya ci tura, hakan yasa ya dinga tafka asarar kudin mota.

Yadda aka kore ni daga bankin da naje neman aiki bayan gano na taba zaginsu a Twitter, Matashi

Wani matashi ya koka bayan bankin Zenith sun ki amincewa su tattauna da shi saboda wata wallafar da yayi shekaru 2 da su ka gabata yana sukar bankin, Legit.ng ta ruwaito.

A cewar mutumin, yayin da yaje a tattauna da shi wurin aikin, wata mata daga bangaren HR ta nuna masa wata wallafa da yayi shekaru biyu da su ka gabata.

Wannan dalilin yasa ya bukaci mutane da su yi taka-tsantsan akan abubuwan da su ke wallafawa a shafukansu. Matashin mai amfani da suna @djbantiben1 ta bayyana artabun da su ka yi bayan Zenith Bank sun ki ba shi gurbin aiki saboda wani wallafa da yayi a Twitter shekaru biyu da su ka gabata.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da saƙo ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you