LabaraiKannywoodRukayya Dawayya zata angwance da angon ta Afakallahu

Rukayya Dawayya zata angwance da angon ta Afakallahu

-

- Advertisment -spot_img

Fitacciyar jarumar masana’antar fina-finann Hausa ta Kannywood Ruƙayya Umar Santa wacce aka fi sani da ruƙayya Dawayya zata angwance da Shugaban hukumar tace finafinai ta jihar Kano, Isma’ila Na’abba Afakallahu.

Ta wallafa katin gayyata a shafin ta

Wani katin gayyata data wallafa a shafin ta na Instagram kwana uku da suka wuce ya nuna cewa yau juma’a, 04 ga watan Nuwamban nan da muke ciki, da misalin ƙarfe biyu na rana ne za’a ɗaura auren jaruma Ruƙayya Dawayya da angon nata a masallacin  dake nan cikin birnin Kano.

Baya ga wannan kuma, jarumar ta ƙara wallafa wani ɗan takaitaccen bidiyo na gayyatar ɗaurin auren wanda kuma aka wallafa shi a gidan talabijin na NTA a shafinta na Instagram daga baya bayan nan.

Ruƙayya Dawayya da Afakallahu sun daɗe suna soyayya

Batun soyayya tsakanin jaruma Ruƙayya Dawayya da shugaban hukumar tace fina-finai ta jihar Kano Isma’il Afakallahu ba wai wani sabon batu bane, musamman ma dai ga masu bin jarumar a shafukan ta na sada zumunta zasu riƙa ganin yadda yake yawan wallafa hotunan sa na yabo da makamantansu.

Screenshot 20221104 002234
Afakallahu / Dawayya

Dawayya ta na yawan wallafa hotunan Afakallahu, hotunan ‘ya ‘yanshi da kusan duk wasu abubuwa da suka shafe shi irin su batutuwan siyasa da sauran abubuwa na yau da kullum a shafukan ta na sada zumunta.

Duk da dai ance soyayya tsakanin Ruƙayya Dawayya da Afakallahu ba yanzu aka fara ba. Sun daɗe suna soyayyar su a sirrance ba tare da bayyana ma jama’a ba. Daga bayan nan ne da abun ya matso jarumar ta riƙa bayyana ma jama’a ta hanyar sanya wa a kafafen sadarwar zamani.

Ta buƙaci jama’a suyi musu addu’a

A ƙasan katin gayyatar da ta ɗora a shafin nata na Instagram, Ruƙayya Dawayya ta roƙi waɗanda ba zasu sami damar zuwa ba da su yi musu addu’a ta fatan alkhairi.

“Alhamdulilah muna gayyatar ‘yan uwa da abokan arziki. Idan ba’a samu dama ba, ayi mana addu’a.” Jarumar ta rubuta.

A wani labarin na daban kuma, wata matashiya mai tashe a soshiya midiya ta koka kan yadda ta gaza samun tsayayyen saurayi duk da tarin mabiya da take da su a shafukanta na sada zumunta na zamani. 

Matashiyar mai amfani da suna Ms PuiYi a shafukan sada zumunta ‘yar shekara 24 ta koka kan yadda mutane da dama ke yabawa da irin kyawun da take dashi, amma kuma bata da tsayayyen saurayin da zata yi tarayya dashi a rayuwarta.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da saƙo ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you