Wata fitacciyar mawaƙiya ‘yar ƙasar Saliyo mai suna Swadu Natasha Beckley ta karɓi addinin musulunci, inda ta kuma bayyana cewa ra’ayin ta ne ta karɓi addinin tunda ta ga shi ya fiye mata.
A rana juma’a, 28 ga watan Oktoban da ya gabata ne dai mawaƙiyar ta wallafa a shafin ta na Facebook inda ta sanar da cewar ta koma addinin musulunci.
Sama da shekara ɗaya tana son karɓar musulunci
Ta ƙara da cewar sama da shekara ɗaya tana ta son ta komawa addinin Musulunci, kuma yanzu tunda ta musulunta zata yi ƙoƙarin ganin cewa ta koyi duk abubuwan da suka kamata ta koya, duk da dai cewa akwai abubuwa da yawa da ya kamata ta koya.
“Na karɓi addinin Musulunci a wannan juma’ar. Zanyi bayani nan bada jimawa ba, amma na kai tsawon shekara ɗaya da wata ɗaya ina ƙoƙarin ganin cewa nayi hakan.
“Shi yasa a wannan juma’ar kawai na yanke shawarar hakan. Duk da dai nasan da cewa ba’a dare ɗaya zan koyi komai da ya danganci musulunci ba, amma lallai zanyi iya bakin ƙoƙarina wajen ganin na koyi abubuwan da suka kamata.” inji mawaƙiyar.
An caccaki nawaƙiyar kan yanayin shigar ta
Mutane da dama sun caccake ta kan yanayin shigar ta da yadda take fitowa, sai dai mawaƙiyar tace da da sannu-sannu zata koyi komai da komai da ya kamata ta koya na addinin Muslunci.
“Ku saurara kuji, wannan sabuwar hanya ce dana ɗauka kuma nake sanar daku. Da sannu-sannu ina ƙara koyon yadda ake gudanar da addinin. Amma ina son ku sani cewa, ra’ayin ku ako da yaushe zai zama na ku ne ba nawa ba. Wannan ni ra’ayina ne da na zaɓar kaina don na cigaba da kasancewa a ciki.
Ƙungiyoyin addinin musulunci sun yaba mata
Kungiyoyi da dama na addinin musulunci sun yaba ma mawaƙiyar bisa ƙoƙarin da ta yi na karɓar addinin inda suka riƙon Allah ya tabbatar da ita akan hanya madaidaiciya.
A wani labarin na daban kuma, kunji wani makaho da ya bayyana cewa kyakkyawar matar shi da ya aura, itace da kanta ta nemi auren shi. Ya bayyana cewa a hakan shi ta ganshi kuma ya birgeta.
Adeleke ya ƙara da cewa yana jin daɗin zama da matar shi saboda ya yarda da ita sosai kuma yana samun natsuwa a ran shi a duk lokacin da yake tare da ita, kamar yadda majiyar mu ta legit ta wallafa.
Ya kuma ce a lokacin da ta yanke shawarar ta aure shi, mutane da dama sunyi ƙoƙarin zuga ta akan kada ta aure shi. Matar duk bata maida hankali akan masu faɗa mata kada ta auri shi ba.
Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.
Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:
Ko kuma ku aiko mana da saƙo ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com