LabaraiSojoji sun halaka 'yan ta'addan Boko Haram da dama...

Sojoji sun halaka ‘yan ta’addan Boko Haram da dama a jihar Borno

-

- Advertisment -spot_img

Dakarun sojojin Najeriya sun halaka ‘yan ta’addan Boko Haram da dama a wani bata kashi da suka yi a yankin Banki na karamar hukumar Bama ta jihar Borno.

Jaridar The Cable ta rahoto cewa sojojin wadanda suka fito daga bataliya ta 151 tare da hadin guiwar ‘yan sakai (CJTF) sun afkawa maboyar ‘yan ta’addan a kauyen Gauri a ranar 30 ga watan Oktoba.

‘Yan ta’addan Boko Haram sun kwashi kashin su a hannu a wajen sojoji

‘Yan ta’addan kuma suna amfani da maboyar ta su wajen ajiyar shanun satar da suka kwato.

“Fiye da mutum goma sha biyar aka halaka nan take,” A cewar wata wani soja wanda aka fafata yakin da shi.

“Dole ta sa ‘yan ta’addan suka arce suka bar shanun da suka sace bayan da yawa daga cikin su, suka samu munanan raunika.”

Majiyar ta kuma bayyana cewa sojojin sun halaka wasu daga cikin ‘yan ta’addan da suka arce suka kira karin mayaka.

Sai dai, sojoji biyu sun rasa rayukan su a yayin bata kashin.

‘Yan ta’addan sun karo mayaka akan babura, amma sojojin sun fatattake su bayan an yi bata kashi.” A cewar majiyar

“Mun halaka karin mutum bakwai daga cikin su a fadan da ya sake barkewa, amma abin takaici biyu daga cikin jajirtattun sojojin mu sun kwanta dama yayin da wasu biyar kuma suka samu raunika yayin da suka bi bayan ‘yan ta’addan da suka arce.”

Ba a samu jin ta bakin kakakin hukumar sojojin kasa Onyema Nwachukwu, game da lamarin ba.

ISWAP ta halaka ‘yan ta’addan Boko Haram da dama a wani sabon karon batta

A wani labarin na daban kuma, mayakan ISWAP sun halaka ‘yan ta’addan Boko Haram da dama a jihar Borno.

Kungiyar ‘yan ta’addan ISWAP ta halaka mayakan Boko Haram mutum takwas a jihar Borno a fada da ya barke a tsakanin su.

A cewar Zagazola Makama, wata jarida wacce ta mayar da hankali kan abubuwan dake aukuwa a yankin tafkin Chadi, kungiyoyin ‘yan ta’addan biyu sun fafata ne a ranar Alhamis a yankin Krinowa na Marte

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana raayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you