LabaraiMai siyar da ‘pure water’ ya durkusa yana godiya...

Mai siyar da ‘pure water’ ya durkusa yana godiya ga Ubangiji yayin da ɗiyarsa ta kammala jami’a

-

- Advertisment -spot_img

Wata mata ta yi murnar Kammala jami’a tare da iyayenta da ‘yan uwanta kamar yadda ta bayyana wa duniya, Legit.ng ta ruwaito.

A bidiyon an ga inda ta tafi da gudu ta shiga shagon siyar da ruwan leda inda mahaifinta ke sana’arsa ta rungume shi.

Mahaifin nata cike da farinciki ya durkusa da guiwoyi kasa yayin da yake godiya ga Ubangiji akan ni’imar da yayi masa ta kammala karatu da diyarsa tayi.

A bidiyon wanda ya bazu a kafar TikTok, bayan yayanta ya sanya mata hannu ne tayi gudu zuwa shagon mahaifinta.

An ga inda mahaifin nata ke wakoki na murna har ya kai ga durkusawa kasa don yi wa Ubangiji godiya.

A bidiyon, yarinyar ta bayyana cewa da sana’ar fiyo wota iyayenta su ka dauki nauyin karatunta har ta gama.

An ga inda mahaifiyarta ke murna inda aka ga wata yarinya tana siyar wa kwastomomi ruwan, ta yuwu kanwarta ce.

2023: Sai ubangiji ya hukunta mu idan bamu goyi bayan Tinubu ba -CAN reshen jihar Legas

Shugabannin kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen jihar Legas, sun bayyana goyon bayan su ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.

Shugaban kungiyar na jihar Reverend Stephen Adegbite, shine ya bayyana hakan a ranar Lahadi 16 ga watan Oktoba. Jaridar Legit.ng ta rahoto.

Za su fuskanci fushin ubangiji idan ba su goyi bayan dan takarar ba

Adegbite yace ubangiji zai hukunta kungiyar addinin idan ta kasa goyon bayan Tinubu a zaben 2023.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you