LabaraiZaben 2023: Kashim Shettima ya bayyana lokacin da za...

Zaben 2023: Kashim Shettima ya bayyana lokacin da za su tuntubi Kwankwaso

-

- Advertisment -spot_img

Dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Sanata Kashim Shettima, ya bayyana lokacin da zai tuntubi dan takarar jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP), Dr Rabiu Musa Kwankwaso.

Kashim Shettima yace zai tuntubi dan takarar ne a lokacin da ya dace kafin zuwan babban zaben shekarar 2023 dake kara matsowa. Jaridar Daily Trust ta rahoto.

Kashim Shettima, wanda yake bayar da lakca a wajen taron limaman birnin tarayya Abuja a ranar Juma’a a matsayin daya daga cikin bakin da aka gayyata, yana ba’a ne ga tsohon dan majalisar tarayya, Garba Ibrahim Muhammad, wanda ya wakilci Sanata Kwankwaso a wurin taron.

Kashim Shettima na ganin kimar Kwankwaso

“Nayi alkawarin ba zan yi maganar cin mutunci akan sanata Rabiu Musa Kwankwaso ba a gabadaya lokacin zabukan nan. Shugaba ne nagari sannan Insha Allah za mu zauna tare sannan mu fahimci juna a daidai lokacin da ya dace nan bada dadewa ba.”

“Wadanda suke shirin raba kasar nan ba za suyi nasara ba, sannan a saboda haka yakamata mu yi hakuri da junan mu sannan mu yi sadaukarwa,” A cewar Kashim Shettima.

Ko a bara an gudanar da irin wannan taron

Tunda farko a yayin jawabin sa, shugaban kwamitin ‘Committee of the FCT Imam Initiative (CFII)’, Imam Tajuddeen Bello, yace taron ya samu wakilcin limamai daga dukkanin jihohi 17 na Kudancin kasar nan wanda aka yiwa taken: “Limamai’ Hadin kai domin cigaban kasa.”

Yace an shirya irin wannan taron a shekarar da ta gabata domin limaman jihohi 19 na Arewacin kasar nan.

Yadda rigima ta barke tsakanin Kashim Shettima da Omoyele Sowore a wajen rattaba hannu kan zaman lafiya

An samu hargitsi tsakanin Kashim Shettima da Omoyele Sowore a wurin rattaɓa hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a tsakanin ƴan takarar shugaban ƙasa na jamiyyu daban-daban da za su fafata a babban zaɓen 2023 dake tafe.

Taron wanda aka yi a ɗakin taron ƙasa da ƙasa (ICC) a Abuja ranar Alhamis, 29 ga watan Satumba, wanda kwamitin zaman lafiya na ƙasa ya shirya sannan ya samu halartar kusan dukkanin ƴan takara na jamiyyu face Asiwaju Bola Tinubu na jamiyyar APC. 

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana raayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you