LabaraiYaro Dan shekara 15 ya kashe mahaifiyar shi kan...

Yaro Dan shekara 15 ya kashe mahaifiyar shi kan hana shi shaye-shaye

-

- Advertisment -spot_img

Wani yaro ɗan shekara 15 dake zaune a ƙauyen Osubeng, gundumar Kwahu dake gabashin ƙasar Ghana ya kashe mahaifiyar shi sakamakon hana shi shaye-shaye da take yi.

Yadda yaron ya kashe mahaifiyar tashi

Ance yaron mai suna Illiasu Amuni ya kashe mahaifiyar tashi mai suna Sakina Amuni ne dai ta hanyar buge ta da sanda sannan kuma ya yanka wuyan ta da wuƙa a yayin da take tsaka da aiki a gonar ta.

Wakilin majiyar mu ta Adom News wanda ya bibiyi labarin yadda abun ya samo asali ya bayyana cewa dama can baya yaron ya sha alwashin cewa lallai sai ya kashe mahaifiyar tashi saboda ta hana shi shaye-shayen tabar wiwi.

Ya amsa laifin da ya aikata

‘Yan uwan yaron dama sauran al’umma basu ɗauki barazanar da yaron yayi da muhimmanci ba har sai da yazo ya aikata wannan ɗanyen aiki.

A lokacin da ‘yan sanda suka iso, sun tasa ƙeyar wanda ake tuhuma inda ‘yan sandan suka ce ya amsa laifin shi na kashe mahaifiyar tashi.

Shugaban ƙauyen da wannan mummunan lamarin ya faru Nana Agyei Debrah Sasu yace kashe mahaifiyar shi da yaron yayi bai zo mishi da mamaki ba, sabili dama yaron ya taɓa yunƙurin sanya mata guba a cikin abinci.

Shaye-shayen miyagun ƙwayoyi ne sila

Nana Agyei dai ya alalaƙanta faruwar mummunan lamarin ga shaye-shayen miyagun ƙwayoyin da matasan suka duƙufa akai inda yayi kira ga iyaye akan su sanya idanun akan yaransu domin kauce ma faruwar irin hakan a gaba.

A wani labarin na daban kuma, kunji cewa Fitacciyar jarumar fina-finan Hausa Ruƙayya Umar Santa wacce aka fi sani da Ruƙayya Dawayya ta buɗe katafaren gurin gyaran jiki na mata a Kano.

Bikin ƙaddamar da wannan guri data buɗe ya samu halarta mutane da dama daga ciki da wajen masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood waɗanda suka zo don taya murna da kuma yin fatan alkhairi ga jarumar.

Jaruma Dawayya dai ta ƙaddamar da wannan katafaren guri ne dai data sanya ma suna ‘DY Utrat 85’ a ranar Laraba 26 ga watan Oktoban nan da muke ciki, a titin Guda Abdullahi dake Farm center a birnin Kano, kamar yadda Mujallar Fim ta wallafa.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da saƙo ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you