LabaraiKano: Yadda rashin wutar lantarki yasa ƴan matan Kuntau...

Kano: Yadda rashin wutar lantarki yasa ƴan matan Kuntau su ka tafi yajin aikin zance

-

- Advertisment -spot_img

Yayin da yankuna da dama da ke cikin Jihar Kano ke fama da matsalar rashin wuta, samari da dama na gwagwarmayar ganin cewa sun kawo mafita saboda yadda ‘yan matansu su ka dena fito musu zance.

Anguwar Kuntau wani yanki ne da ke karamar hukumar Gwale a Jihar Kano, kuma tsawon lokaci tun da su ka shiga duhu har yanzu ba a samu mafita ba.

Daga cikin ‘yan matan yankin, ta shaida wa wakilin Dala FM yadda su ka dena fita zance soro saboda rashin wuta don za su cutu kwarai saboda sauro da duhu.

Akwai wadanda kuma wayoyinsu ne su ka mutu, hakan yasa su ka yanke alaka da samarin nasu duk da cewa ba haka rai yaso ba.

Tsofaffi kuwa har fita zanga-zanga su ka yi don ganin rashin dacewar duhun da aka sa su, don yanzu haka wasu ba sa samun damar bacci sai dare.

Tuni samari su ka zagara don ganin cewa sun kawo mafita akan wannan gagarumar matsalar da ke yunkurin raba su da ‘yan matansu.

Kawo yanzu dai KEDCO ba ta kawo sabuwar transformer ba, amma ana sa ran wannan koken zai yi aiki, ta yadda gwamnati ko kuma masu hannu da shuni za su duba wannan lamari don su kawo taimakon gaggawa.

Wani matashi ya hallaka dan uwan sa har lahira saboda rashin biyan kudin wutar lantarki

Wani matashi ya harbe yayan sa bisa rashin biyan kudin wutar lantarki a Uruagu, karamar hukumar Nnewi ta Arewa a jihar Anambra, kudu maso gabashin Najeriya.

Ya zargi dan uwan sa da yanke masa wuta

Rahotanni sun bayyana cewa wanda ake zargin, Peter Orji, ya zargi babban yayansa, Godwin Orji, da dage masa wutar lantarkin sa.

Lamarin ya faru ne a ranar Talata.

Ya kasa biyan kudin wutan gidan sa

An dai ce wanda ake zargin ya kasa biyan kudin wutan bangaren sa har Naira 1,500 duk wata, wanda hakan ya sa wanda hakan ya tunzura wanda aka kashe ya yanke wutan gidan kanin nasa.

Wanda ake zargin ya fusata wanda hakan yasa ya tunkari dan uwan sa.

Rikici ya barke tsakanin ‘yan uwa biyu

PREMIUM TIMES ta samu labarin cewa, sakamakon rikicin da ya barke tsakanin ‘yan uwa biyu, wanda ake zargin ya afka dakinsa, tare da dauko bindiga ya harbe dan uwansa inda nan take ya ce ya ce ga garinku.
“Abinda ya faru shine tuntuni dama akwai ‘yar tsama tsakaninsu. Sun dade suna samun sabani a kan fili,” wani mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa PREMIUM TIMES.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you