LabaraiKisan Ummita: Yadda shari'ar tuhumar da ake wa dan...

Kisan Ummita: Yadda shari’ar tuhumar da ake wa dan kasar Chana ta kaya

-

- Advertisment -spot_img

Dan kasar Chanan nan Geng Quangron da ake tuhumar sa da kisan budurwar sa ‘yar Kano, Ummulkulsum Sani Buhari wacce akafi sani da Ummita ya musanta aikata laifin zargin da ake tuhumar sa da shi.

Mista Geng ya bayyana hakan ne a gaban babbar kotun jihar Kano mai lamba 17 da ke a Miller Road, yayin da kotun ta ci gaba da sauraren karar da Gwamantin Jihar Kano ta shigar tana zargin sa da kisan Ummulkusum. Rahoton jaridar Aminiya.

Ana dai zargin Mista Geng da kisan Ummita, wacce ta kasance suna soyayya da juna, inda ya bita har unguwar su dake Janbulo ya shiga har cikin gidansu ya caccaka mata wuka, wanda hakan yayi sanadiyyar rasa ranta har lahira.

An nemo wanda zai yi masa fassara

A baya an sami tsaiko a sauraren shari’ar sakamakon rashin wanda zai yiwa wanda ake zargi fassara, bisa la’akari da cewa yana daga cikin hakkinsa a yi masa sharia da harshen da ya fi fahimta.

A zaman kotun na ranar Alhamis, mai gabatar da kara, Kwamishinan Shari’a na jihar Kano, Barista Musa A. Lawan ya gabatar wa kotun wanda zai yi aikin fassarar wanda kuma dan asalin kasar Chana ne mai suna Mista Guo Cumru.

Takardar da mai gabatar da kara ya karanta na cewa:

“A ranar 16 ga watan Satumba, kai Mista Geng da ke zaune a rukunin gidajen da ke unguwar Railway a jihar Kano ka je wani gida a unguwar Janbulo a Jihar Kano inda ka kashe wata budurwa mai suna Ummulkusum Sani Buhari ta hanyar caccaka mata wuka a wurare daban-daban na jikinta.”

“Laifin da ake zargin ka da aikatawa dai ya saba da sashe na 221 a cikin kundin Pinal Kod.”

Sai dai Mista Geng Quanron ya musanta aikata laifin da ake zargin sa da shi.

An bukaci a daga sauraron karar

Mai gabatar da kara ya nemi kotun da ta daga shari’ar zuwa ranar 14 zuwa 16 ga watan Nuwamba don su gabatar da shaidunsu.

Sai dai lauyan wanda ake tuhuma Barista Muhamamd Balarabe Danazumi bai amince da wannan ranaku ba, inda ya shaida wa kotu cewa ranakun ba su yi masa daidai ba.

Sai dai mai gabatar da kara ya roki kotun da ta yi la’akari da cewa mai yin fassarar yana zuwa ne daga birnin tarayya Abuja.

Alkalin kotun, mai shari’a Sanusi Ado Ma’aji, ya dage shari’ar zuwa ranar 16 da 17 da 18 ga watan Nuwamban 2022.

Yadda dan Chana ya yaudari Ummita cewa ya musulunta -Babbar kawarta

Wata ƙawar Ummukulsum Sani Buhari (Ummita) matashiyar nan da Geng Quanrong ya halaka a Kano, ta bayyana cewa ya yaudari marigayiyar da cewa ya musulunta domin ta aure shi.

Daily Trust ta rahoto cewa Quanrong yanzu haka yana garƙame a hannun ƴan sanda bisa halaka Ummita a gidan iyayenta a ranar Juma’a. Ummita da Quanrong masoya ne

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you