LabaraiYadda magidanci ya lakadawa jaririn sa dukan tsiya saboda...

Yadda magidanci ya lakadawa jaririn sa dukan tsiya saboda ya hana shi barci

-

- Advertisment -spot_img

Hukumar kare hakkin dan Adam ta kasa (NHRaC) da kungiyar mata ‘yan jarida (NAWOJ) reshen jihar Imo, sun yi kira ga gwamnatin jihar da hukumar ‘yan sanda da su gaggauta cafke tare da hukunta wani magidanci mai suna Mr Conidence Amatobi, bisa zargin lakadawa jaririn sa mai wata biyu a duniya shegen duka.

Mr Amatobi ya bugi jaririn mai suna Miracle da abin makale kaya na roba wanda yayi sanadiyyar karyewar hannun jaririn saboda ya hana shi ya samu barci mai dadi. Jaridar News Direct ta rahoto.

Dukan da aka yiwa jaririn ya sanya sai da aka yanke masa hannu

Lamarin ya sanya sai da aka yanke karyayyen hannun jaririn a babban asibitin tarayya dake a birnin Owerri na jihar.

Da take bayyana yadda lamarin ya auku, mahaifiyar Miracle mai suna Mrs Favour Chike, mai shekara 20 a duniya wacce ta fito daga kauyen Idemili na jihar Anambra, tace ta bar jaririn da mahaifin sa domin zuwa bandaki a ranar Juma’a 7 ga watan Oktoban 2022, lokacin da lamarin ya auku.

Favour ta bayyana cewa ta jiyo karar jaririn yana kuka wanda hakan ya sanya tayi sauri domin sanin dalilin da yasa yake tsala kuka, kawai ta ci karo da hannun jaririn na dama ya kumbura kuma kashin ya karye saboda duka da mahaifin sa yayi masa.

Amatobi, ya amsa cewa jaririn ya hana shi barci da kukan da yake yi wanda hakan ya sanya yayi masa dukan tsiya domin yayi masa shiru

“Bayan ya fahimci cewa ya karya masa hannu, yayi amfani da itace da robali domin daidaita karyayyun kasusuwan,” Inji ta

“Da nayi masa magana kan abinda yayi, sai ya kulle mu a cikin daki domin kada na gayama mutane halin muguntar da ya aikata ko na nemi taimako. Ya kwace wayar hannuna don kada na kira makwabta.”

Ta kuma bayyana cewa bayan ta samu ta fita daga gidan, ta kai jaririn asibitin kauyen amma sai suka ki duba shi kafin daga bisani ta tafi babban asibitin tarayya dake Owerri inda anan ne aka ya ke hannun jaririn.

Mahaifiyar yaron tayi kira da gwamnati ta kawo mata dauki

Mahaifiyar jaririn ta bukaci da a taimaka mata ta ceto rayuwar jaririnta inda tayi kira ga gwamnatin jihar da sauran kungiyoyin kare hakkin dan Adam da su taimaka mata ta samo wa jaririn ta adalci.

Shugabar kungiyar ‘yan jarida mata reshen jihar Imo, Mr Dorathy Nnaji, wacce ta gana da ‘yan jarida bayan ta ziyarci jaririn a asibitin inda aka yanke masa hannu, ta tabbatar da cewa raunin da mahaifin yaron yaji masa shine silar da ta sanya aka yanke masa hannu.

Magidanci na ta lalata da ‘ya ‘yanshi mata bayan rabuwa da mahaifiyar su

Wani magidanci dai yayi ta cigaba da yin lalata da ‘ya’yanshi ‘yan mata su biyu tun bayan rabuwa da yayi da mahaifiyar su wani lokaci can baya.

Kwamishiniyar walwala da jin ɗaɗin mata ta jihar Anambra tace an kama wani magidanci mai suna Nwobi, mai matsakaitan shekaru bisa tuhumar cewa yana lalata da ‘ya’yanshi mata su biyu; da mai shekara uku da kuma ‘yar shekara biyar.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da saƙo ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com


Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you