LabaraiKotu ta tura wani matashi gidan kaso bisa damfarar...

Kotu ta tura wani matashi gidan kaso bisa damfarar wata tsohuwa miliyoyin kudade

-

- Advertisment -spot_img

Wata babbar kotun jihar Kano ta yankewa wani matashi mai suna Aminu Ishaq hukuncin shekara uku a gidan kaso bisa amfani da kudin haram.

Alkali mai shari’a Nasiru Saminu shine ya zartar da wannan hukuncin a ranar 25 ga watan Oktoban 2022.

Da jikan tsohuwar aka hada baki wajen yin satar

Matashin da aka yankewa hukuncin yana daya daga cikin matasa shida da aka cafke a satar sama da Naira miliyan sha biyar (N15,000,000m) daga asusun wata tsohuwa wacce kaka ce ga daya daga cikin su (Al-Mustapha Nasir). Shafin LIB ya rahoto.

Kotun da yankewa Al-Mustapha Nasir hukunci a ranar 6 ga watan Oktoban 2022.

Matasan sun shiga hannun hukuma ne bayan an shigar da wani korafi wanda yayi zargin cewa Al-Mustapha Nasir ya sace layin wayar kakar sa, ya hada baki da abokan sa inda suka sace sama da N15m daga asusun ajiyar ta na banki ta hanyar turawa daga banki da kuma cirewa a POS.

Tuhumar da ake masa na cewa:

“Kai Aminu Ishaq, wani lokaci a shekarar 2021 a Kano, bisa ikon wannan kotun ka rike kudin da suka kai N350k, wanda kasan kudin sata ne, hakan yasa ka aikata laifin da ya cancanci hukunci a bisa sashi na 17 (a) da (b) na dokar kafa hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta shekarar 2004.”

Ya amsa laifin da ake tuhumar sa da shi

Wanda ake karar ya amsa laifin da ake tuhumar sa da shi bayan an karanta masa.

Bisa la’akari da afuwar da matashin ya nema, Salihu Sani, lauyan dake kara ya nemi kotun da ta yanke masa hukuncin da ya dace. Lauyan dake kara wanda aka kara, Nuriyyah Musa ta nemi kotun da ta yi sassauci wurin yankewa matashin hukunci.

Alkali Saminu ya yankewa matashin hukuncin shekara uku a gidan kaso da zabin biyan tarar Naira dubu dari (N100,000).

Kotun daukaka kara tayi watsi da tuhumar da ake wa Nnamdi Kanu, shugaban ‘yan ta’addan IPOB

Wata kotun daukaka kara mai zamanta a birnin tarayya Abuja ta wanke shugaban haramtacciyar kungiyar ‘yan ta’adda, Indigenous People Of Biafra (IPOB), Mazi Nnamdi Kanu.

Gwamnatin tarayya na tuhumar Nnamdi Kanu a babban kotun tarayya dake Abuja, bisa laifuka 15 da suka hada da tawaye da ta’addanci, laifukan da ake zargin ya aikata a lokacin da yake gangamin jagorantar ‘yan aware

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you