LabaraiShekaru kaɗan bayan auren makauniya, shi ma ya makance,...

Shekaru kaɗan bayan auren makauniya, shi ma ya makance, danginsa sun juya masa baya

-

- Advertisment -spot_img

‘Yan uwan wani mutum su na ta zundensa bayan ya fada tarkon soyayyar wata mata mai cutar makanta kamar yadda Legit.ng ta ruwaito.

Mutumin wanda asali daga Arusha yake, cikin kasar Tanzania, yana tsaka da neman halaliyarsa sai ya hadu da wata makauniya wacce yaji kaf duniya babu wacce tayi masa sai ita.

Mutumin mai suna Rashidi Apahamanyi Musasigye ya bayyana kudirinsa na auren Lilian.

Wannan lamarin ya bai wa Lilian mamaki inda taga mutumin da ba ya da wata nakasa ya bukaci ya zabe ta a matsayin matarsa, kamar yadda Afrimax English ta bayyana.

Anan ne Lilian ta bayyana wa Rashidi labarin yadda mijinta ya bar ta bayan sun haifi yara biyu ba tare da sake waiwayarta ba. Hakan bai da Rashidi ya sauya niyyarsa ba, anan ne yace mata yana son rayuwa da ita har karshen rayuwarsa.

‘Yan uwansa sun nuna masa cewa bai dace ya aureta ba, zai fi kyau idan har ya auri wacce za ta iya tallafa masa maimakon mai nakasa.

Duk da haka, sun yanke shawarar yin aurensu inda su ka ci gaba da rayuwa cikin soyayya da kauna. Sai dai bayan shekaru kadan aka kusa halaka Rashidi ba tare da ya yi komai ba, wanda daga bisani kuma aka tura shi kurkuku.

Bayan wani lokaci kadan ya makance. Rashidi ya zargi ‘yan uwansa da yi masa mugun aikin, inda yace ba su da niyyar ganin ya ci gaba.

Yar uwata ce ta yi mini asiri na makance saboda mai kudi ya yi alkawarin zai aure ni – Makauniya

Wata mata ‘yar kasar Ghana mai fama da larurar makanta, da aka bayyana sunanta da Portia Ama, ta bayyana labarinta marar dadin ji kan yadda aka yi mata asiri da ya sanya ta tsinci kanta cikin wannan hali na makanta.

Matar wacce ke zaune a wani kauye a yankin Central Region, ta zargi cewa ‘yar uwarta ce ta yi mata asiri saboda tana kishi akan wani mai kudi da ya yi mata alkawarin zai aureta a lokacin da tana ‘yar shekara 13 a duniya.

A wata hira da Ama ta yi da D.J Nyame na gidan talabijin din SVTV, ta yi zargin cewa ‘yar uwartan wacce a da take bautawa gumaka, ta sha alwashiin ganin ba ta samu nasarar auren wannan mutumi mai arziki ba, hakan ya sanya ta mai da hankali wajen ganin ta lalata mata rayuwa, inda ta shiga yi mata asiri har sai da ta ga ta makanta ta.

A cewarta ta ziyarci Fastoci da dama don ganin idonta ya dawo amma duka kokarin da take a banza.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayinku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: hello@labarunhausa.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you