LabaraiMasu garkuwa da mutane sun afka masallaci, sun halaka...

Masu garkuwa da mutane sun afka masallaci, sun halaka rai tare da sace dan kasuwa da dansa

-

- Advertisment -spot_img

Masu garkuwa da mutane wanda yawan su yakai mutum 10 sun farmaki wani masallaci a Jalingo, babban birnin jihar Taraba.

Masu garkuwa da mutanen sun halaka mutum daya sannan suka sace wani dan kasuwa tare da dansa a yayin harin da suka kai a masallacin.

An bayyana lokacin da harin ya auku

Jaridar Daily Trust ta tattaro cewa masu garkuwa da mutanen sun farmaki masallacin ne wanda yake a kwanar Jalo cikin unguwar Saminaka a Jalingo lokacin Sallar Magriba.

Yaron dan kasuwar da aka dauke dai dalibi ne a wata makarantar sakandire ne dake a yankin.

An addabi mutanen yankin da hare-hare

A cikin ‘yan watannin da suka gabata dai masu garkuwa da mutane sun halaka mutane ciki har da dan sanda sannan sun sace sama da mutum 30 a yankin.

Masu garkuwa da mutanen wanda ke gudanar da ayyukan su daga tsaunikan dake kusa da rafin Lamurde a karamar hukumar Ardo_Kola, sun tilasta mutane da dama yin kaura daga yankin.

Har ya zuwa lokacin kammala hada wannan rahoton, ba a samu jin ta bakin kakakin hukumar ‘yan sandan jihar Taraba, DSP Usman Abdullahi, ba.

Bayan karbar N6m kudin fansa, masu garkuwa da mutane sun bani N2000 nayi kudin mota -Cewar matar da aka sace

A wani labarin na daban kuma, wata matar da aka yi garkuwa da ita ta bayyana yadda masu garkuwa da mutane suka bata N2000 tayi kudin mota bayan karbar N6m kudin fansa.

Wata mai bayar da shaida, Hajiya Fatima Ibrahim, ta gayawa wata babbar Kotu a Zaria cewa wadanda suka yi garkuwa da ita sun bata N2000 a matsayin kudin mota bayan sun karbi N6m a matsayin kudin fansa.

‘Yan sanda na karar Dalhatu Shehu, Lawal Aliyu-Bullet, Nuhu Ismaila da Nura Usman da laifukan fashi da makami, mallakar makamai ba bisa ka’ida ba da kuma garkuwa da mutane. 

Hafsat brahim tana bayar da shaida ne a matsayin shaidar mai kara a zaman da kotun ta dawo don cigaba da sauraron karar a babbar kotu dake Dogarawa, Zaria.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you