LabaraiMuna nan kan bakar mu, ba za mu taɓa...

Muna nan kan bakar mu, ba za mu taɓa karɓar IPPIS ba – ASUU

-

- Advertisment -spot_img

Ƙungiyar malaman jami’o’i ta ƙasa wato ASUU tace har yanzu tana nan a kan bakan ta na cewar ba zata yarda da tsarin IPPIS da gwamnatin Najeriya ta zo da shi ba wajen biyan lakcarori albashin su da sauran kuɗaɗe.

Mataimakin shugaban ASUU ya bada bayani

Mataimakin shugaban hukumar na ƙasa Chris Piwuna ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a lokacin da yake tattaunawa da jaridar premium times ta tuwita.

Ya kuma ƙara da cewa duk da ƙoƙarin da kakakin majalissar wakilai yayi wajen ganin an biya malaman jami’o’i kuɗaɗen su da aka riƙe, har yanzu dai babu wani malamin da aka biya ko sisi.

Alƙawuran da suke so a cika musu

Ƙungiyar malaman jami’o’i ta ASUU dai ta shiga yajin aiki ne a watan Fabrairun wannan shekarar biyo bayan gazawar gwamnati wajen cika musu wasu alƙawura da aka ɗauka a baya.

Alƙawuran da ASUU take so a cika mata sun haɗa da wasu sauye-sauye a wajen biyan albashi da alawus ɗin malaman, ƙarin kuɗaɗe da ake tura ma jami’o’i, sai kuma sabon tsarin biyan ma’aikata mai suna UTAS da jami’o’i suka zo da shi saɓanin na IPPIS.

Sai dai ita gwamnati a nata ɓangaren tace yin amfani da hanyoyin biyan albashi sama da ɗaya zai janyo ƙarin kashe wasu kuɗaɗen waɗanda ba dole bane gwamanti ta iya kashewa.

A tattaunawar tashi da premium times, mataimakin shugaban hukumar ASUU Piwuna yace lallai matsayar da suka ɗauka kan IPPIS ba zata sauya ba.

“Ba zamu karɓi tsarin IPPIS ba duk ta yanda aka juya shi, ba zamu taɓa amfani da tsarin a makarantun mu ba.” inji shi.

Muna son jami’o’i su ci gashin kansu

“Samun ‘yancin cin gashin kan jami’o’i shine abinda ke gaban mu ba wai abubuwan dake cikin IPPIS ba. Daga ofishin shugaban ma’aikata na gwamnatin tarayya ake tafiyar da ayyukan jami’o’i da shuwagabannin su. Mu kuma burin mu shine su cire hannayen su daga hidindimun jami’o’i.”

Ya kuma ƙara da cewar ASUU zata cigaba da bibiyar matakai na shari’ah dangane da yajin aikin da kotu ta sanya suka janye. Zasu yi ƙoƙarin gamsar da kotu cewa su suna mutunta duk hukuncin da ta yanke.

A wani labarin kuma, kunji cewa jami’an tsaron Najeriya sun yi nasarar cafke wasu mutane su biyu dake yima waɗanda ba ‘yan Najeriya ba katin ɗan ƙasa a sansani ‘yan gudun hijira a jamhuriyar Nijar.

Haɗakar jami’an tsaron farin sojoji da na Imagireshin da kuma na hukumar ‘yan sanda ne dai suka yi nasarar waɗannan masu rijistar katin ɗan ƙasa na bogi a jamhuriyar Nijar kamar yadda Dailytrust ta wallafa.

Kamar yadda jami’an tsaro suka bada bayanan, an kama waɗanda ake tuhuma ne a sansanin ‘yan gudun hijira dake Gagamari a cikin jamhuriyar ta Nijar. An kama su ne da laifin yima waɗanda ba ‘yan Najeriya ba katin ɗan ƙasa, suna sanya su a cikin ma’adanar bayanan Najeriya.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da saƙo ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you