Labarai'Yan kwankwasiyya kadai nake yima waƙa - Tijjani Gandu

‘Yan kwankwasiyya kadai nake yima waƙa – Tijjani Gandu

-

- Advertisment -spot_img

Fitaccen mawaƙin nan na masana’antar Kannywood Tijjani Gandu wanda kuma yayi fice a waƙoƙin siyasa dana yabon manzon Allah S.A.W ya bayyana cewa ‘yan ɗariƙar Kwankwasiyya kaɗai yake yima waƙa.

Da waƙar Abba Gida-gida nayi suna

Ya bayyana hakan ne a wata hira da yayi da mujallar Fim, inda ya bayyana cewa da waƙoƙin ‘yan kwankwasiyya yayi tashe musamman ma dai waƙar Abba gida gida wacce tayi fice a zaɓen 2019.

Ya ƙara da cewar shi dama kowa yasan cewa mawaƙin kwankwasiyya ne musamman ma dai a cikin Kano. A saboda da haka babu wani ɗan siyasa da zai yi ma waƙa face ɗan ɗarikar kwankwasiyya.

Ni mawaƙin kwankwasiyya ne kaɗai

“Kuma ni da man a siyasa ni mawaƙin Kwankwasiyya ne. In dai a Kano ne, babu wani ɗan siyasa da zan yi wa waƙa sai ɗan Kwankwasiyya da ‘yan cikin ta. Kamar yadda ka ji mu na cewa, ba mu fara don mu daina ba!”

Tijjani Gandu ya bayyana cewa bai taɓa tunanin cewa zai koma harkar waƙa ba. Ya bayyana cewa yayi sana’o’i da yawa ciki hada harkokin zane-zane wanda a cikin hakan ne ya ƙulla alaƙa da mawaƙa daga nan har ya fara harkokin waƙa.

Mawaƙin yace yakan je studio na mawaƙa daban-daban domin yayi musu zane wanda a hakan ne suka saba da mawaƙan wanda daga nan ne shima ya rikiɗe ya kama harkar waƙar.

“Da yake ina yin waƙoƙi na Mauludi a makarantar mu, sai ya zama na iya rubutun waƙoƙin yabon Manzon Allah da kuma na faɗakarwa. To sai na fara da na yabon Manzon Allah. Ina yi har aka fara sani na a cikin mawaƙa.” inji Tijjani Gandu.

Waƙoƙin da Tijjani Gandu yayi tashe da su

Tijjani Gandu dai yayi tashe sosai a ‘yan kwanakin baya. Waƙar ‘yar maye ce dai waƙar da aka fi sanin shi da ita, kamar dai yadda ya bayyana ma mujallar Fim. Waƙar Farin wata da waƙar Na Tuba na daga cikin waƙoƙin da aka san Tijjani Gandu da su.

Daga ƙarshe, mawaƙin yayi kira ga abokan sana’ar shi akan su riƙe mutuncin sana’ar tasu, su kuma kiyayi yin duk wani abu da zai zubar da mutuncin su da kuma mutuncin sana’ar tasu.

A wani labarin kuma, fitaccen malamin addinin Muslunci Sheikh Malam Aminu Ibrahim Daurawa ya buƙaci waɗanda suka ɗora hoton amarya shi ana mata kwalliya a soshiyal midiya da suyi maza su goge shi.

Malam Daurawa yace kwalliya ake yi mata a cikin ɗakin mahaifiyar ta, amma aka samu wasu a ciki da suka ɗauke ta hotuna sannan kuma suka yaɗa su a soshiyal midiya.

“Amma wasu daga cikin waɗanda ba’a san ko su waye ba sun shiga har ɗakin babar ta sun ɗauki hoton ta ana yi mata kwalliya, kuma suka zo suna yaɗawa.”

Ya cigaba da cewa yaɗa irin wannan ba abu bane da ya dace, musamman duba da cewa ita matar ba waje ta fito taje ta yi party ba ko wani abu makamancin haka, a cikin dakin mahaifiyarta aka ɗauki hoton.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da saƙo ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you