LabaraiBa tabbas ko mun biya bukatun 'yan Najeriya, sun...

Ba tabbas ko mun biya bukatun ‘yan Najeriya, sun cika burika akan gwamnatin mu -Aisha Buhari

-

- Advertisment -spot_img

Uwargidan shugaban Najeriya Aisha Buhari, ta bayyana cewa bata da tabbas ko gwammatin mijinta ta biyawa ‘yan Najeriya bukatun su saboda yawan burikan da suka ci a kan gwamnatin

Aisha Buhari ta bayyana hakan ne cikin wata tattaunawa ta musamman da BBC cikin harshen turanci, inda tace wannan dalilin ne ya sa ta nemi afuwar ‘yan Najeriya.

Ta bayyana dalilin neman afuwar ‘yan Najeriya

A kwanakin baya Aisha Buhari ta ba ‘yan Najeriya hakuri kan wahalhalu da halin matsin rayuwa da suke fama da shi a yayin addu’o’i na musamman da ta shirya a ranar 1 ga watan Oktoba don bikin cika shekara 62 da samun ‘yancin-kan Najeriya.

A kalamanta:

“Burikan da aka ɗora mana suna da matuƙar yawa. Mutane sun ɗora burika a kanmu, kuma wataƙila bayan shekara bakwai ba mu cika musu dukkan wadannan burikan ba.”

“Allah ne kaɗai ya san abin da ke zuciyar mutane. A matsayinka na ɗan Adam, ba ka da hurumin cewa ka yi daidai, ko kuma ka ce ka yi abin da ya kamata. Saboda haka gwamnatin ta yi ƙoƙari, amma ba lallai haka kowa ke gani ba.”

“A wajensu (gwamnatin) sun yi ƙoƙari, Allah kaɗai ya sani. Saboda haka dole mu bai wa ‘yan Najeriya haƙuri ko da mun cika musu burinsu ko ba mu cika ba.” Inji ta

Tana ganin APC za ta yi nasara a zabe mai zuwa

A farkon watan Oktoban ne jam’iyyarsu ta APC mai mulkin ƙasar ta naɗa Aisha Buhari a matsayin jagorar tawagar kamfe ta mata a matakin takarar shugaban ƙasa.

Ko da aka tambaye ta yaya take gani game da yiwuwar samun nasarar jam’iyyar APC a zabe mai zuwa, Aisha Buhari sai ta kada baki tace:

“Me ya sa za ki yi min wannan tambayar? Tsaf kuwa za mu ci gaba. APC ce za ta ci zaɓe. Da izinin Allah.” A cewar ta.

Aisha Buhari ta nemi afuwar ‘yan Najeriya kan matsalar tattalin arziki da ake fama da shi tun shekarar 2015

Uwargidan shugaban kasar Najeriya, Aisha Buhari a ranar Juma’a, 30 ga watan Satumba, ta nemi afuwar ‘yan Najeriya game da matsalar tattalin arziki da ake fuskanta a fadin kasar tun bayan hawan mijinta kan karagar mulki


Aisha Buhari ta nemi afuwar ne a lokacin da take jawabi a wajen taron sallar Juma’a na musamman da kuma lacca na musamman na ranar samun ‘yancin kai karo na 62.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you