LabaraiTinubu ya bayyana babban dalilin da yasa Atiku yakamata...

Tinubu ya bayyana babban dalilin da yasa Atiku yakamata ya janye ya mara masa baya

-

- Advertisment -spot_img

Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, dan takarar shugaban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar All Progressives Congress (APC), ya nemi abokin hamayyar sa na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) Atiku Abubakar, da ya janye ya mara masa baya a babban zaben shekarar 2023 dake tafe.

Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Litinin 17 ga watan Oktoban 2022, a yayin wani taron tattaunawa da shugabannin yankin Arewacin Najeriya a karkashin inuwar kwamitin hadaka na Arewa a birnin Kaduna. Jaridar Legit.ng ta rahoto.

Tinubu ya bayyana dalilin da yasa ya nemi Atiku da ya mara masa baya

Da yake bayani akan makasudin yin wannan furucin na sa, Tinubu ya nemi Atiku da ya mayar da halaccin da yayi masa lokacin da nemi takarar shugaban kasa a shekarar 2007 a karkashin tsohuwar jam’iyyar Action Congress of Nigeria (ACN), ta hanyar janye kudirin takarar sa ya mara masa baya.

Taron da ake yi da shugabannin yankin Arewacin Najeriya, na daga cikin wata muhimmiyar tattaunawa da ake da wasu zababbun ‘yan takarar shugaban kasa domin tattaunawa da su akan shirye-shiryen da suke da su akan yankin kafin zuwan babban zaben shekarar 2023.

An dai gudanar da taron ne a Arewa House a birnin Kaduna.

Ka taimaka ka goyi bayana domin in cimma nasara – Tinubu ga El-Rufai

A wani labarin na daban kuma, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya nemi gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i da ya goya masa baya domin samun nasara.

Dan takarar shugabancin ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar APC mai mulki, Bola Ahmed Tinubu ya roƙi gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai akan ya goyi bayan shi don ganin ya cimma nasara a zaɓen 2023 dake gabatowa.

Tinubu yadai yi wannan roƙon ne a lokacin da yake jawabi a wajen taron tattalin arziƙi da kasuwanci da ya gudana ranar Asabar a Kaduna, kamar yadda majiyar mu ta Vanguard ta wallafa.

Da yake jinjina ma gwamnan, Tinubu yace Najeriya na buƙatar shugaba mai kaifin basira irin su Nasiru El-Rufai

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da saƙo ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you