IlimiKungiyar ASUU ta janye yajin aikin wata 8 bisa...

Kungiyar ASUU ta janye yajin aikin wata 8 bisa sharadi

-

- Advertisment -spot_img

Kungiyar malaman dake koyarwa a jami’o’i (ASUU), ta janye yajin aikin da ta kwashe watanni takwas tana yi.

Kungiyar ta ASUU ta janye yajin aikin ne a bisa wani sharadi kamar yadda wani mamba na kwamitin zartarwa na kasa na kungiyar ya shaidawa Channels TV da safiyar ranar Juma’a.

Shugabannin ASUU sun tattauna

ASUU ta yanke shawarar janye yajin aikin ne a yayin wani zama da tayi na shugabannin ta wanda ya fara a daren ranar Alhamis zuwa safiyar ranar Juma’a.

kungiyar ta kira zaman ne domin samar da matakin gaba da zata dauka bayan rassanta na jihohi sun zauna akan hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke satin da ya gabata

Kotun daukaka kara ta umurci ASUU da ta janye yajin aikin kafin ta saurari karar da ta daukaka kan umurnin da aka ba malamai masu koyarwa a jami’a na su koma bakin aikin su.

Mambobin kwamitin zartarwa na kasa na kungiyar, wadanda suka hada da shugabannin kungiyar na jihohi, da shugabannin kungiyar na kasa, suka halarci zaman da akayi a sakatariyar kungiyar ta ASUU dake birnin tarayya Abuja.

Kungiyar ta dai tsunduma yajin aiki tun ranar 14 ga watan Fabrairun wannan shekarar.

Kwanan nan yajin aikin ASUU zai zo karshe -Femi Gbajabiamila

A wani labarin na daban kuma da muka kawo muku, kakakin majalisar wakilai Femi Gbajabiamila ya bayyana cewa yajin aikin ASUU na daf da karewa.

Kakakin majalisar wakilai ta Najeriya, Femi Gbajabiamila yayi tsokacin cewa yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i ASUU keyi wanda yaki ci yaki cinyewa na daf da zuwa karshe.

Femi Gbajabiamila ya bayyana cewa yajin aikin zai kare nan da ‘yan kwanaki kadan masu zuwa. Jaridar Vanguard ta rahoto.

Kakakin majalisar wakilai ta tarayyan ya bayyana hakan yayin da yake gayawa shugabannin kungiyar yadda ta kaya a ganawar da yayi da shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Litinin

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

WhatsApp Group

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you