LabaraiKotun daukaka kara tayi watsi da tuhumar da ake...

Kotun daukaka kara tayi watsi da tuhumar da ake wa Nnamdi Kanu, shugaban ‘yan ta’addan IPOB

-

- Advertisment -spot_img

Wata kotun daukaka kara mai zamanta a birnin tarayya Abuja ta wanke shugaban haramtacciyar kungiyar ‘yan ta’adda, Indigenous People Of Biafra (IPOB), Mazi Nnamdi Kanu.

Gwamnatin tarayya na tuhumar Nnamdi Kanu a babban kotun tarayya dake Abuja, bisa laifuka 15 da suka hada da tawaye da ta’addanci, laifukan da ake zargin ya aikata a lokacin da yake gangamin jagorantar ‘yan aware. Rahoton Channels TV.

Alkalai uku na kotun sun ce kotun tarayyar bata da hurumin yi masa shari’a bisa la’akari kan yadda aka kamo shi aka dawo da shi Najeriya ta hanyar leta ka’idojin dawo da mai laifi zuwa kasar sa na OAU.

Abinda kotun daukaka karar tace kan tuhumar da ake wa Nnamdi Kanu

Kotun tace laifuka 15 da ake tuhumar Kanu da su, ba su bayyana wuri, rana, lokaci da kuma yanayin laifukan da ake zargin sa da su kafin dawo da shi Najeriya ba bisa ka’ida wanda hakan ya sabawa yarjejeniyar kasashen duniya.

Kotun ta kuma kara cewa gwamnatin tarayya ta kasa fadin inda aka kamo Nnamdi Kanu duk kuwa da girman laifukan da ake tuhumar sa da su.

Kotun tayi nuni da cewa yadda aka kamo Nnamdi Kanu da dawo da shi Najeriya daga kasar Kenya ba tare da bin doka ba, hakan keta masa ‘yanci ne.

Ta kara da cewa kotun tarayyar bata duba yadda aka samo da gabatar da Nnamdi Kanu a gaban ta ba, kafin fara yi masa shari’a.

Duba sa cewa kotun tarayyar ta kasa yin gamsashshen bayani kan kalubalantar hurumin da take da shi musamman kan batun kamo Kanu da dawo da shi Najeriya daga kasar Kenya, kotun ta kasa fahimtar cewa za a iya kamfani da iznin kamu ne kawai a cikin Najeriya. Cewar hukuncin kotun daukaka karar.

Shugaba Buhari ya bayyana hanya ɗaya tilo da zaa bi wajen sako Nnamdi Kanu

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya ƙara jaddada matsayar sa kan cewa kotu ce kaɗai za ta iya wanke Nnamdi Kanu, shugaban ƙungiyar ‘yan awaren ƙabilar Ibo ta IPOB. Jaridar Punch ta rahoto.

Shugaba Buhari ya bayyana hakan ne yayin da yake mayar da martani kan roƙon da sarakunan yankin kudu maso gabas su kayi masa na ya saki Nnamdi Kanu a wajen taron da su kayi da shugaban ƙasan a ranar Juma’a a birnin Abakaliki na jihar Ebonyi, yayin ziyarar aiki ta kwana biyu da ya kai jihar.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you