LabaraiASUU ta magantu kan hukuncin kotu, ta bayyana matakin...

ASUU ta magantu kan hukuncin kotu, ta bayyana matakin da zata dauka

-

- Advertisment -spot_img

Kungiyar malaman jami’a ASUU ta bayyana cewa tana tattaunawa domin sanin matakin da zata dauka kan hukuncin da kotu ta yanke akan yajin aikin da take yi.

Kotu ta umurci kungiyar ta ASUU da ta koma bakin aiki yayin da ake cigaba da sauraron daukaka karar da kungiyar tayi kan hukuncin da kotun ma’aikata ta yanke.

Kungiyar na nazari kan hukuncin kotun

Da yake tattaunawa da jaridar Vanguard, shugaban kungiyar ta ASUU, Prof. Emmanuel Osodeke, yace jagororin kungiyar da tawagar lauyoyin su za su nazarci hukuncin kafin daukar matakin su na gaba.

Muna tattaunawa da neman shawarwari akan lamarin, idan muka kammala, za mu dauki matakin da ya dace, amma a yanzu tattaunawa muke kan lamarin.

Sai dai an samo cewa an kira taron yanki-yanki na kungiyar sannan kuma nan ba da dadewa ba za a gudanar da taron masu gudanarwa NEC na kungiyar domin samar da matakin da za a dauka na gaba.

Kotu ta umurci ASUU ta koma bakin aiki

Kotun daukaka kara a ranar Juma’a ta umurci kungiyar da ta bi umurnin da kotun ma’aikata ta yanke kafin tayi wani abu kan karar da kungiyar ta daukaka.

Idan ba a manta ba dai, kungiyar ASUU ta tsunduma yajin aiki tun 14 ga watan Fabrairun wannan shekarar bisa wasu bukatun su, sannan gwamnatin tarayya ta yiwa wasu sabbin kungiyoyin jami’o’i rajista domin su rika fafatawa da ASUU.

Ina matuƙar jin zafin yajin aikin da ASUU ke yi -Shugaba Buhari

A wani labarin na daban Kuma, shugaba Buhari yace yajin aikin da ASUU ke yi na matukar sosa masa rai.

Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari yace yana jin raɗaɗin zafin cigaba da yawaitar samun tsaikon da ɓangaren ilmin gaba da sakandire ke samu a ƙasar nan.

Haka kuma shugaba Buhari yayi kira ga ƙungiyar malaman jami’a ASUU da ta janye yajin aikin ta na wata bakwai, sannan a buɗe makarantu yayin da ake cigaba da tattaunawa don ganin an biya musu buƙatun da ba su fi ƙarfin gwamnati ba

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you