Ana tsaka da wani taro a garin Abuja, aka nemi wayar Namadi Sambo aka ga ta yi layar zana kamar yadda LIB ta ruwaito.
Sanata Shehu Sani ya bayyana hakan a wata wallafar da yayi a shafinsa na Twitter. Sani ya ce duk da yawan jami’an tsaro a wurin amma sai da wani barawo ya lallaba ya sace wayarsa.
Lamarin ya faru ne a ranar 6 ga watan Oktoba yayin wani taro na kaddamar da littafin tarihin rayuwar marigayi Gwamna Solomon Lar.
Kamar yadda Sani ya bayyana, ana tsaka da taron aka nemi wayar aka rasa, ashe har barayin sun yi aikinsu sun gama.
Gwamnatin tarayya zata kara kashi 5% na haraji kan kiran wayan salula
Nan ba da dadewa ba ‘yan Najeriya za su fara biyan harajin kashi 12.5 na ayyukan sadarwa a daidai lokacin da gwamnatin tarayya ke shirin kara harajin kaso biyar wanda ya hada da ayyukan sadarwa a Najeriya.
Hukumar sadarwa ta shirya taro
Ministar kudi da tsare-tsare ta kasa, Zainab Ahmed ce ta bayyana haka a wani taron masu ruwa da tsaki kan aiwatar da haraji kan ayyukan sadarwa a Najeriya ranar Alhamis a Abuja.
Hukumar Sadarwa ta Najeriya NCC ce ta shirya taron.
Za a kara kashi 5% akan wanda ake biya a da
Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya bayar da rahoton cewa, za a kara biyar akan kashi 7.5 na haraji da ake biya a da wato VAT, kan ayyukan sadarwa.
Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa
Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:
Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com