LabaraiPDP ba zata taba barin satar dukiyar talakawa ba...

PDP ba zata taba barin satar dukiyar talakawa ba -Lai Mohammed

-

- Advertisment -spot_img

Ministan watsa labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed, yace ba zai taba yiwuwa ba jam’iyyar PDP ta sauya daga dabi’arta ta satar kudaden kasa ba idan har ta sake samun damar komawa kan mulki.

Ministan ya bayyana Hakan ne a yayin wata hira da kamfanin dillancin labarai na Nigeriya (NAN) a ranar Alhamis a birnin Arusha na kasar Tanzania.

Lai Mohammed na tsokaci ne kan rahotannin da ke cewa wasu daga cikin ‘yan kwamitin gudanarwa na jam’iyyar PDP na kasa sun dawo da N122.4 miliyan da shugaban jami’iyyar ya tura musu. Jaridar Daily Trust ta rahoto.

Akwai rahotannin da ke yawo cewa shugaban jam’iyyar PDP na kasa Iyorchia Ayu, ya biya sama da N100 miliyan ga ‘yan kwamitin bayan kammala zaben fidda gwani na jam’iyyar.

Lai Mohammed yace:

Idan mutum zai iya yiwa kan sa sata, zai yiwa sauran mutane sata ba tare da shakku ba.

Matsalar itace jam’iyyar PDP ba zata taba sauyawa ba, sannan kamar yadda ake cewa ba a sauyawa tuwo suna.

Lokacin da PDP ta Fadi zabe a shekarar 2015, sun amice cewa sun gane kurakuren su, Amma a bayyane yake ba su koyi darasin komai ba.

Allah ya kiyaye, idan har suka sake samun lalitar al’umma, ba za su bar ko Kobo ba.

Mun San abinda muka tarar lokacin da muka amshi mulki a 2015, har yanzu korafi muke akan hakan.

Muna fatan ‘yan Najeriya, yanzu sun ga irin niyyar da suke da ita idan suka karbe madafun iko.

Lai Mohammed ya nemi da PDP da tayi bayanin inda ta samo kudaden

Lai Mohammed yace dole ne a yi wasu tambayoyi kan lamarin ciki har da ko meyasa tunda farko aka biya irin wannan kudin Kuma wannan ne kawai karo na farko.

Ya kuma ce yakamata a tambayi jam’iyyar yadda aka yi ta samo wadannan kudaden.

Lai Mohammed yace a lokacin da yake mamba a kwamitin gudanarwa na ACN da APC, ba kudin da aka biya zuwa asusun sa.

Ban taba tuna cewa wasu irin kudade, kowane iri sun taba shiga asusun Wani mamba na kwamitin gudanarwa na ACN ko APC ba.

2023: Dalilin da yasa PDP zata lashe zaɓen shugaban ƙasa -Atiku Abubakar

Ɗan takarar kujerar shugaban ƙasa a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar People’s Democratic Party (PDP) a babban zaɓen shekarar 2023, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana cewa jam’iyyar sa zata iya lashe zaɓen shugaban ƙasa mai zuwa.

Atiku Abubakar ya bayyana hakan ne a jihar Gombe bayan ya ƙaddamar da ofishin yaƙin neman zaɓen sa a jihar

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you