LabaraiAmotekun ta kama 'Yan achaɓa 80 a jihar Ondo

Amotekun ta kama ‘Yan achaɓa 80 a jihar Ondo

-

- Advertisment -spot_img

Aƙalla mutane 80 ‘yan achaɓa ne rundunar jami’an tsaro na musamman na jihar Ondo suka ce sun kama saboda dalilin rashin bin dokar hana zirga-zirga ga ‘yan achaɓa da aka sanya a jihar.

Gwamnatin Ondo ta hana ‘yan achaɓa aikin dare

A watan daya gabata ne dai gwamnatin jihar ta Ondo ta ƙaƙaba dokar hana zirga-zirga ga ‘yan achaɓa daga ƙarfe shida na yamma zuwa ƙarfe shida na safe (6pm – 6am) a kowace rana. Haka nan jami’an sun haramta ma gidajen casu kaiwa dare da yawa sabili da ba’a yadda wani ya kwana a gidan casu ba.

Vanguard ta wallafa cewa kwamandan rundunar ta Amotekun wato mista Adetunji Adeleye ya zargi ‘yan achaɓa da cewar ayyukan su na ƙara taimakawa wajen ta’azzarar miyagun laifuka a jihar. Ya bayyana hakan ne bayan gudanar da samame kan ‘yan achaɓa a Akure babban birnin jihar.

Aƙalla mutane 80 ne yan kabo-kabo da jami’an na Amotekun suka kama a babban birnin jihar. Shugaban hukumar yace wannan samamen anyi shi ne domin kakkaɓe wasu miyagu masu mummunar manufa akan jihar.

jamiaan amotekun
Amotekun/Punch

An yadda jami’an tsaro su hau babura

“Mutanen da aka yadda su hau babura da dare  sune jami’an tsaro da kuma ma’aikatan dake ayyuka na musamman waɗanda suma dole ne su riƙa yawo da shedar gurin aikin nasu a yayin hawa babur a cikin lokacin dokar.

“Mun fahimci cewa ‘yan achaɓa ne manya masu janyo aikata manyan laifuka a duk faɗin jihar. Saboda haka, zuwa ƙarfe bakwai na yamma mutanen mu zasu koma kan duk wasu mahaɗan hanyoyi da kuma cikin gari don gudanar da aiki.

“Babu maganar hawa babur da dare, duk wanda aka kama yana hawa babur da dare za’a ɗauka cewa ko mai laifi ne kuma za’a ɗauki mataki akan shi daidai da hakan.

An hana zuwa gidan casu da daddare

“Babu maganar zuwa gidan casu da dare, dole ne duk wanda yaje gidan casu ya bar gidan kafin dare ya raba, domin kuwa babu wanda zai ƙara kwana a gidan casu. Mun shirya tsaf wajen ganin mun fatattaki duk wasu nau’o’i na miyagun ayyuka a jihar.” inji kwamandan na Amotekun.

Shin kunji cewa An saki ragowar fasinjojin jirgin ƙasa na hanyar Abuja-Kaduna da aka yi garkuwa da su? A yammacin Laraba ne dai muka samu labarin bkuɓutar ragowar fasinjojin jirgin ƙasa da ‘yan ta’adda suka kwashe a jirgin ƙasa a hanyar Abuja zuwa Kaduna a watan Maris na shekarar 2022.

Jaridar Punch ta wallafa cewa ragowar fasinjojin jirgin ƙasar waɗanda mutum 23 da uku ne sun samu kuɓuta da yammacin yau Laraba da misalin ƙarfe huɗu na yamma (4pm).

Shugaban hukumar tsaron soji ta ƙasa Janar Lucky Irabor ne ya shaidawa manema labarai ta wata takarda batun kuɓutar ragowar fasinjojin jirgin su 23. Ya bayyana cewa jami’an sojoji ne suka yi ƙoƙari wajen samun nasarar kuɓutar da mutanen da suka ɗaɗe a hannun ‘yan ta’addan.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da saƙo ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you