LabaraiKannywoodShin kun san yaushe ne bikin Ruƙayya Dawayya da...

Shin kun san yaushe ne bikin Ruƙayya Dawayya da Afakallahu?

-

- Advertisment -spot_img

Batu akan ko yaushe ne bikin jaruma Ruƙayya Umar wacce aka fi sani da Ruƙayya Dawayya, wacce kuma ta kasance mai tsara fina-finai a masana’antar Kannywood da kuma shugaban hukumar tace fina-finai ta jihar Kano, wato Isma’il Na’abba Afakallahu dai abune da mutane da dama suka ƙosa su sani.

Soyayya tsakanin Ruƙayya Dawayya da Afakallahu ba baƙon abu bane

Maganar soyayya dai tsakanin jaruma Ruƙayya Dawayya da kuma Isma’il Afakallahu ba wani sabon batu bane, inda duk wani mai bibiyar jarumar a shafukan sada zumunta musamman ma dai na Instagram da Tiktok zai dinga ganin alamun hakan.

Jarumar ta kasance tana yawan wallafa hotunan Afakallahu, hotunan ‘ya ‘yanshi da kusan duk lamurran da suka shafe shi irin su lamurran siyasa da sauran abubuwa na yau da kullum a shafukan ta na sada zumunta.

Majiyar mu ta mujallar Fim ta bayyana cewa batun soyayya tsakanin Ruƙayya Dawayya da Afakallahu abune da aka ɗaɗe ana gudanar wa cikin sirri. Sai dai abubuwa suka kankama ne jarumar ta fara bayyana wa duniya cewa akwai alaƙa ta soyayya tsakanin ta da shugaban hukumar tace fina-finan.

Screenshot 20221005 152324
Ruƙayya Dawayya

Daga yanzu zuwa kowanne lokaci za’a iya ɗaura auren

Majiyar tamu ta ƙara da cewa ta samu bayanai daga majiya mai ƙarfi kan cewa maganar auren Dawayya ya riga da ya matso sosai. Ana sa ran cewa daga yanzu zuwa kowanne lokaci za’a iya ɗaura auren.

Wasu da Mujallar Fim ɗin ta tattauna da su, sun bayyana cewa akwai yiwuwar ba wani taro za’a yi ba wajen bikin. Sai dai sun bayyana cewa lallai sai sunyi taro, sunyi shagali saboda a cewar su, Dawayya ba ƙaramar mace bace.

Sun ƙara da cewa haɗin Afakallahu da Ruƙayya Dawayya yayi daidai sosai, inda suka ƙara da cewa da zarar sun kammala shirye-shiryen da suke kai a yanzu, zasu bayyana ma jama’a ko yaushe ɗaurin auren ba tare da wani ɓata lokaci ba.

A kwanakin baya-bayan nan ne dai aka ga jarumar ta matsa ƙaimi wajen wallafa hotuna da kuma abubuwan da suka jiɓanci masoyin nata a shafukan sada zumunta musamman ma dai Tiktok da Instagram. A watan Yulin da ya gabata, jarumar ta wallafa wani hoto na Afakallahu haɗe da wani rubutu mai ɗaukar hankali.

Samun Afakallahu Allah ne ya amsa addu’atah

Samun masoyi na gaskiya a wannan zamanin da rashin gaskiya yayi yawa sai ƙarfin addu’ah. Alhamdulillahi ya rabbi lakal hamdu wash shukur. Allah na gode maka da ka amsa addu’atah. Khairun nasa man yan fa un nass.”

Screenshot 20221005 152224 1

Al’umma da dama a ciki da wajen masana’antar ta Kannywood sun bayyana murnar su sosai akan wannan batu na auren jaruma Ruƙayya Dawayya da kuma Isma’ila Na’abba Afakallahu da ake shirin yi.

A labarin mu na baya, mun kawo muku cewa hukumar zaɓe ta fitar da jerin sunayen ƴan takarar gwamna a zaɓen 2023. Hukumar zaɓe ta ƙasa mai zaman kanta  INEC, ta fitar da jerin sunayen ƴan takarar zaɓen 2023 na kujerun gwamna tare dana ƴan majalissun jihohi da zasu fafata a kakar zaɓen dake ta ƙara gabatowa.

Hukumar dai ta fitar da jerin sunayen ne a ranar Talata inda a ciki aka ga cewa sunayen ƴan takarar da suke da rigingimu na cikin jam’iyya, ko kuma batutuwa na shari’a da suke a gaban kotubasu samu damar shiga cikin jerin ƴan takarar na zaɓen 2023 ɗin ba kamar yadda majiyar mu ta Tribune ta wallafa.

Sai dai wannan mataki da hukumar zaɓen ta ɗauka na ƙin sanya sunayen ƴan takara masu rigingimu ya tada ƙura sosai. Wasu magoya bayan su nuna ƙin amincewar su kan wannan mataki na hukumar zaɓen. Idan aka duba za’a ga cewa lokaci yanzu ya kusa ƙure ma ƴan takarar da abin ya shafa.

A jihar Ogun, ƴan takara 13 suka nuna sha’awar neman kujerar gwamna. Sunayen guda 12 daga cikinsu sun shiga cikin jerin da hukumar zaɓe ta fitar. Daga ciki akwai gwamna mai ci kuma ɗan takarar gwamna a jam’iyyar APC wato gwamna Dapo Abiodun.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da saƙo ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you