37.1 C
Abuja
Tuesday, March 28, 2023

ASUU : Kotu ta umarci ASUU da ta janye yajin aikin

IlimiASUU : Kotu ta umarci ASUU da ta janye yajin aikin
ASUU
kotu ta umurci ASUU da ta janye yajin aiki

A yau Laraba ne kotun masana’antu ta Najeriya ta umarci kungiyar malaman jami’o’i da ta janye yajin aikin da ta shafe watanni tana yi a fadin kasar nan.

Jaridar PUNCH ta rahoto cewa ASUU ta tsunduma yajin aiki tun ranar 14 ga watan Fabrairu domin neman a biya su hakkokin su da suka hada da inganta jami’o’i, nazarin albashin malaman jami’o’i da dai sauransu.

An yi ta zaman ganawa tsakanin gwamnati da Mambobin kungiyar ta ASUU sai dai har yanzu an kasa cimma matsaya.

Sakamakon haka gwamnatin tarayya ta garzaya kotu domin kalubalantar yajin aikin.

Kamar yadda shafin jaridar TheCable ya ruwaito, gwamnatin ta bakin lauyanta, James Igwe, ya roki kotun da ta dakatar da ASUU daga cigaba da yajin aikin, har zuwa lokacin da za a yanke hukunci kan karar.

Cikakkun bayanai daga baya…

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Ku duba wasu labaran mu

Check out other tags:

Labaran da suka fi tashe