25.1 C
Abuja
Thursday, March 23, 2023

Tabarar da mata masu yabon ma’aiki ke yi ta zarce ta masu rawar TikTok da ‘yan fim, Fantimoti

LabaraiTabarar da mata masu yabon ma’aiki ke yi ta zarce ta masu rawar TikTok da ‘yan fim, Fantimoti

Fitacciyar mawakiyar finafinai a baya, yanzu haka kuma sha’ira a fannin yabon manzon Allah SAW, Maryam Fantimoti ta ce tabarar da mata sha’irai masu yabon ma’aiki su ke yi, ta fi ta ‘yan rawar TikTok da ‘yan fim.

Kamar yadda ta shaida wa Freedom Radio Kano, ta ce dangane da shigarsu ta fitar da surarsu, cakudewa tsakanin maza da mata da suke yi ya munana.

A cewarta:

Abinda yasa nayi magana akan na hadarar manzon Allah SAW shi ne yadda ake yawan korafi akan yabon manzon Allah a gyara. Na daya a gyara alkaluma. Na biyu a gyara harshe, sannan a gyara dabi’a ta sha’irai.

Saboda mu mata ne. Wata sha’irar idan ki ka kalleta sa’ar ‘yar da na haifa ce. Za ki samu ta yi shiga irin ta su ta yara.

Ya kamata a gyara. Ina ganin kuma duk abinda ake yi yayin yabon manzon Allah SAW in dai ya saba wa dabi’a to ina tunanin wannan abin ya yi muni.

A bangaren wata sha’irar ta ce sam ba haka bane. Bai dace a yi wa sha’irai kudin goro ba.

Batun shiga ce, yanayin waka da cakuduwa tsakanin maza da mata. Kuma hukumar tace finafinai tana iyakar kokarinta wurin tantance wakoki tare da tace su.

Ta ce yanzu haka dai an dena samun irin wadannan matsalolin.

Wata budurwa mai rawar TikTok a masallaci ta faɗa komar ƴan sanda

Ƴan sanda a birnin Islamabad na ƙasar Pakistan sun cafke wata budurwa mai amfani da manhajar TikTok bisa laifin tiƙar rawa a masallaci.

An kama budurwar ne tare da ƴan tawagarta a ranar Litinin bayan bidiyonta tana rawa a masallacin Faisal ya ƙaraɗe shafukan sada zumunta. Jaridar Islamic Information ta rahoto.

Limamin masallacin ya kai ƙorafi akan budurwar

Limamin masallacin Mohsin Ishaq shine ya shigar da ƙorafi akan budurwar da ƴan tawagarta a ciki har da mai ɗaukar bidiyon, a ofishin ƴan sanda na Margalla bisa tanadin dokar PPC 295-A.

A cikin ƙorafin na sa ya bayyana cewa yaga wani bidiyo a shafukan sada zumunta na wata budurwa ba sanye da kallabi ba kuma cikin shiga mara kamala. Kwatsam kawai sai ta shiga cikin harabar masallacin na Faisal inda ta keta rigar mutuncin wurin ibadar.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Ku duba wasu labaran mu

Check out other tags:

Labaran da suka fi tashe