27.5 C
Abuja
Thursday, March 23, 2023

A gado daya muke kwana: Yadda tagwaye su ka dirka wa mace daya ciki, tana gab da haihuwa

LabaraiA gado daya muke kwana: Yadda tagwaye su ka dirka wa mace daya ciki, tana gab da haihuwa

Wasu tagwaye sun janyo cece-kuce bayan sun bayyana yadda su ke kwanciya da mace daya kuma yanzu haka su na shirin tarbar jaririnsu don ta kusa haihuwa, Legit.ng ta ruwaito.

A gado daya su ke kwana kullum kamar yadda su ka bayyana. Kuma wannan lamarin ne yafi bai wa kowa mamaki.

A wani bidiyo da Nicholas Kioko ya saki a shafinsa ba Youtube, tagwayen sun bayyana irin rayuwar soyayyar da su ke yi da matarsu.

Teddy da Peter sun bayyana cewa su na gab da zama iyaye kuma ba su riga sun yi aure ba tukunna amma su na kiranta da matarsu.

Kamar yadda Teddy yace:

“Mu da matarmu ne muka zama. Kuma mun yanke shawarar aurenta ne kasancewar mu tagwaye. Yanzu haka a daki daya muke kwana.”

Sun bayyana yadda su ka hadu a coci wanda daga nan ne su ka yi musayar lambar waya da ita.

Dama Kuma Peter ba ya da waya a lokacin don haka yana amfani da wayar dan uwansa ne.

Yayin da aka tambayeta ko cikin wanene a jikinta, ta ce bata sani ba, hakan yasa su biyun su ka amince dan ya zama nasu.

Wani Likita a kasar Saudiyya ya gana da wasu tagwaye da ya raba shekaru 13 da suka gabata

‘Yan biyun lokacin da aka haife su an haife su ne a manne da juna a kasar Saudiyya. Yawancin gabobin jikinsu kamar su hanji da mafitsara suna hade ne wuri daya.
Abdallah Al-Rabiah, babban mai kula da Cibiyar Bayar da Agajin Gaggawa ta Sarki Salman (KSrelief), ya gana da Hassan da Mahmoud a ranar Laraba wadanda a da sassan jikin su yake a hade. ‘Yan asalin kasar Masar ne, amma mazauna birnin Riyadh, kimanin shekaru 13 kenan bayan da aka yi nasarar raba su a wani aikin tiyata da aka yi musu a garin Riyadh.

Likitoci a asibitin King Abdulaziz Medical City sun yi wa tagwayen tiyata a shekarar 2009 a lokacin da suke da watanni 9 kacal. An hade su a cikin ciki kuma an raba wasu gabobin jiki da sassan jiki, ciki har da hanji da kuma fitsari.

Al-Rabiah ya ce masarautar za ta ci gaba da zama fitila ga mabukata da marasa galihu a duk fadin duniya. Shirin likitancin da aka raba Hassan da Mahmoud, wani karin girma ne na ayyukan jin kai na kasar, in ji wanda ake gudanarwa a karkashin umarnin Sarki Salman da Yarima mai jiran gado Mohammed bin Salman na kasar Saudiyya.

Tagwayen dai sun samu rakiyar iyayensu ne a ziyarar da suka kai babban birnin kasar Saudiyya, inda suka gode wa jama’a da gwamnatin kasar Saudiyya bisa shirya yi wa ‘ya’yansu tiyata. Lafiyar yaran ya inganta a tsawon shekaru, in ji su.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayinku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausaagmail-com

Ku duba wasu labaran mu

Check out other tags:

Labaran da suka fi tashe