Wani magidanci, Rasheed Afeez ya maka matarsa a gaban kotun Ibadan inda yake bukatar a raba aurensu saboda matarsa ba ta barinsa ya kwanta da ita, Daily Trust ta ruwaito.
Afeez, wanda ma’aikacin banki ne kuma malamin makarantar firamare, ya bayyana cewa tun kafin aurensu su ka yi gwajin jini amma kwatsam sai ta dena barinsa ya hada shimfida daya da ita.
A kara da cewa:
“Yanzu haka Nafisat yawon bin otal iri-iri take yi.” Yayin mayar da martani, Nafisat wacce ma’aikaciyar asibiti ce, sannan tana da yara biyu, ta amince a raba aurensu mai shekaru tara saboda Afeez yana damunta da jaraba.”
Ta ci gaba da cewa:
“Mai girma mai shari’a ya mayar da ni kamar ‘yar tsana, kusan kullum neman mu kwanta ba tare da ya duba illar hakan ga lafiyarmu yake yi.
“Bai damu da halin da nake ciki ba, kawai son kai ne da shi. Idan naki amincewa sai ya tursasa ni kwanciya da shi.
“Akwai daren da Afeez ya bukaci mu kwanta duk da mun yi fada. Ni kuma naki amincewa daga nan ne yaso ya tursasa ni, na yi sauri na tsere kicin inda ta dauki wuka don in kare kaina.
“Sannan ina tsoron ci gaba da haihuwa da shi saboda kada in haifi mai lalurar sikila. Don daya daga cikin yaranmu yana fama da cutar. Daga ni har Afeez duk AS ne. Bai damu da siya wa danmu da ke fama da lalurar magani ba.”
Ta ci gaba da bayyana rashin sanin mutuncin kansa da yake yi, don a cewarta ba ya daukar dawainiyar matarsa da ta yaransa.
Alkalin kotun, Mrs S. M Akintayo ta dage sauraron karar zuwa ranar 12 ga watan Satumba.
Yadda na hadu da mijin da na aura a Otal din da na raka saurayina lokacin ina budurwa, Matar aure
Wata mata ta bayyana yadda su ka hadu da mijin da ya aureta yayin da ta fita shakatawa tare da tsohon saurayinta a shafinta na Facebook , LIB ta ruwaito.
Matar mai suna Millicent Nwanyimarania ta bayyana yadda ta hadu da mijin a shekarar 2016 yayin da ta raka saurayinta otal don amsar wasu takardu.
A cewarta ta tsaya gefen wurin wanka ne tana jiransa kawai sai ta hango wani hadaddan saurayi ya tunkarota. Tun a lokacin ta ji ta fada tarkon soyayyarsa.
Ta ci gaba da cewa:
“Ya fara da tambayata yadda nake tare da tambayar idan ina tare da wani ne. Ni kuma na shaida masa cewa na raka wani dan uwana ne wanda yaje ganin wani.”
Ta shaida yadda su ka tsinke da hira har yana sanar da ita daga garin da yake ita ma ta shaida masa nata garin. Ta ce duk ta kosa ya amshi lambarta.
Ta ci gaba da cewa:
“Muna musayar lamba sai saurayina ya fito mu ka tafi. Mutumin nan ya kwashe tsawon lokaci bai kirani ba har kawayena su na zolayata akan cewa kila ma ko ajiye lambata be yi ba.”
Ta ce bayan wata daya ne mutumin ya kira ta inda ya shaida mata cewa tafiya yayi shiyasa be kirata ba.
Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayinku a wajen sharhi dake kasa
Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:
Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: hello@labarunhausaagmail-com