34.9 C
Abuja
Monday, March 20, 2023

Jiya nayi mafalkin Buhari ya rike hannuna mun shiga Aljannah, Sirajo Sa’idu Sokoto

LabaraiJiya nayi mafalkin Buhari ya rike hannuna mun shiga Aljannah, Sirajo Sa'idu Sokoto

Wani matashi dan asalin Jihar Sokoto kuma dan gani-kashenin Buhar, Sirajo Sa’idu Sokoto ya bayyana wani mafalki mai nan al’ajabi da yayi wanda ya janyo masa cece-kuce a Facebook.

A cewarsa, jiya ya kwanta bacci inda yayi mafalki da shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari.

Ya ce ya yi mafalkin ya shiga Aljanna tare da shugaban kasa Muhammadu Buhari kuma a cewarsa, Buharin ne ya rike hannunsa.

Kamar yadda yayi wallafar:

“Jiya na yi mafalkin Buhari ya rika hannuna mun shiga Aljannah.”

Ba wannan bane karon shi na farko da yayi makamanciyar wallafar ba, akwai lokacin da yayi addu’ar Allah ya tarwatsa shirin duk masu son juya wa Buhari baya.

Bayan kwanaki kadan ‘yan bindiga su ka je su ka yi garkuwa da ‘yan uwansa da yawa a kauyensu da ke Sokoto.

Bayan nan ne yayi wata wallafa inda yace ya bar shekar Buhari, sakamakon sace ‘yan uwansa da aka yi.

A wannan karon ma, mutane sun dinga caccakarsa. Ga wasu daga cikin tsokacin jama’a karkashin wallafar tashi:

Abba Salisu Kasco Tsanyawa yace:

“Aljannah ta duniya ko ta lahira????

Daga duniya har lahira wlh babu wata alfarma da wannan tsohon zeyimaka

Kaima rashin sanin darajar kai da ciwon kai yasa kake tunanin wani Dan Adam zai kama hanunka zuwa gidan aljannah.”

A Sadeeq Jibreel Abdullahi yace:

“Baka kula sosai bane hanyar wuta ce kuka bi.”

Yusuf Sai Ta’allah yace:

“Yadda kasa Buhari arai kadaura masa so da Annabi kake yi wa haka da shi za kai mafarki ka ga da ka more.”

Abdu Danyaro Wudil yace:

“Kai wato kana karya ta hadisin manzon Allah ko.ai tunda shugaba bane shi kafin ya shiga Aljanna sai Allah ya tambayeshi.”

Bayan hukuncin kisa, ina fatan Abdulmalik Tanko ya mutu ba musulmi ba, Sirajo Sa’idu Sokoto

Wani ma’aboci amfani da kafar sada zumuntar zamani ta Facebook, Sirajo Sa’idu Sokoto ya yi wallafa mai zafi dangane da makashin Hanifa Abubakar, dalibarsa.

Dama an kwashe watanni ana ta faman shari’ar Abdulmalik har ta kai ga a wasu mutanen su na ganin dakyar a dauki matakin da ya dace akan shi musamman ganin daga bisani ya musanta kisan da yayi.

Sai dai a jiya, 28 ga watan Yuli ne kotu ta yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya wanda hakan ya sa mutane da dama cikin farin ciki.

Amma duk da haka wasu suna ganin bai dace ya mutu yana musulmi ba, sun yi masa fatan kafirta kafin a karasa masa hukuncin da yayi daidai da abinda ya aikata.

Sirajo Sa’idu Sokoto yana daya daga cikin wanda su ka dauki zafi dangane da lamarin inda har yayi wata wallafa wacce ta dauki hankalin mutane.

Kamar yadda ya rubuta a shafinsa:

“Ina yiwa Abdulmalik Tanko Fatan ya mutu ba musulmi ba.”

Wannan wallafar ta tayar da kura, har wasu suna ganin menene yayi zafi da yake wannan fatan.

LabarunHausa ta tsinto wasu daga cikin tsokacin jama’a karkashin wallafar ta Sirajo:

Jabeer Abdullahi yace:

“Subhanallah, wannan kuskure ne,shi musulmi ne laifine yayi ba shirka ba. Kuma Allah Yana iya yafe mai..”

Umar Saleh ya yi tsokaci inda yace:

“Dole sai ka nunawa duniya kai ba a saka a makaranta ba ko kuma an saka ka ki yi. Zamanin Annabiمُحَمَّد ﷺ an kashe wata baiwar Allah sai wani bawan Allah ya aibata ta shi kuma mai gidannamuﷺ ya ce tayi tuban da za a rabawa mutanan madina sahabba’i guda 70 in ban mantaba ya ishesu.”

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: hello@labarunhausa.com

Ku duba wasu labaran mu

Check out other tags:

Labaran da suka fi tashe