27.5 C
Abuja
Wednesday, March 22, 2023

” Ba zan aura maka ‘ya ta ba idan har baka da ra’ayin mace tayi aiki”  – Inji wata uwa a martanin ta ga wani sako da aka ce mace mai aiki ba matar da za’a aura ba ce

Ilimi" Ba zan aura maka 'ya ta ba idan har baka da ra'ayin mace tayi aiki"  - Inji wata uwa a martanin ta ga wani sako da aka ce...

Wata uwa yar Najeriya ta mayar da martani ga wani sako da aka wallafa a shafin  Tuwita, wanda wanda a cikin sa aka  ce mace mai aiki, ba matar da za’a aura bace. 

Dan asalin Arewacin Najeriya ne ya fadi wannan kalamai

Wani  ma’abocin shafin tuwita mai shafin  @Galadima_Samaru ,daga arewacin Najeriya, shine  ya yi wannan bayani a shafin sa na Tuwita , Inda  yake cewa, ” ba zai yiwu mace mai aiki ta rike gida ba.” 

Ga kalaman sa:

“Babu yadda mace mai son aikin zata   zama mace ta gari da kuma uwa. Sam hakan ba  zai yiwu ba. Gidaje  da yawa sun tarwatse,  saboda mata masu ra’ayin yancin kai na yammacin turai, sun yadda cewa suna da haƙƙin suyi aiki,  kuma a lokaci guda suna sarrafa gidan  aure, har ma kuma su zama uwa.

Ita dai gaskiya daya ce.Kuyi  duba a tsanaki ga al’ummomin yammacin duniya a yau, zaku ga dukkanin su tarkace ne, saboda matan su, sun yi watsi da nauyin da ke kansu wanda Allah ya dora musu,  saboda  neman daukakar duniya.”

Ita mace ce mai aiki kuma yayan ta ma dole suyi aiki

Da take mayar da martani,  wacce ita ma ’yar Arewacin Nageriya ce, ta ja wa  maza masu irin wannan tunanin kunne da  su guji zuwa neman auren  ’ya’yanta mata guda  biyu.

A cewarta,

 

“ita tsohuwar ma’aikaciyar banki ce, wacce a yanzu haka ta mallaki makaranta, kuma tana son daya daga cikin ‘ya’yan ta; ta zama likita yayin da ta biyun kuma take fata ta zama  lauya , kuma ba ta son maza masu irin wannan tunanin su zo neman auren wadannan ‘ya’ya nata.”

Hukuma ta yi ram da wanda ya kona mazaunan ‘yar aikin gidansa da dutsen guga mai zafi

Rundunar ‘yan sandan Jihar Imo sun kama wani Uzoma Egbema bayan ya yi amfani da dutsen guga mai zafi wurin kona mazaunan ‘yar aikin gidansa, Chimkamso Ekeocha, mai shekaru 12 bisa zarginta da tuka keken yaransa.

An kama mutumin ne da taimakon wani mai rajin kare hakkin bil’adama, Darlington Chidera Ibekwe bayan labarin ya yadu a kafafen sada zumunta.

Wakilin Daily Trust ya tattaro yadda yanzu haka wanda ake zargin yake Sabon ofishin ‘yan sanda da ke Owerri.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, CSP Mike Abattan, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ya ce za a mayar da mutumin bangaren binciken masu laifi na musamman don daukar matakin gaba.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

WhatsApp Group

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Ku duba wasu labaran mu

Check out other tags:

Labaran da suka fi tashe