
Kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta bayyana jarabawar da ake yi a jami’ar jihar Kaduna (KASU) a matsayin saba ka’ida da ka’idojin gudanar da jarabawar a makarantun ilimi.
Kungiyar ta bayyana hakan ne ta wata sanarwa da ta fito daga shiyyar Kano, inda ta dage cewa duk wani jarrabawar da aka gudanar a halin yanzu dole ne a sake gudanar da shi domin tabbatar da karko.
A ranar 2 ga watan Agusta ne jami’ar ta koma harkokin ilimi tun ranar 14 ga watan Fabrairu lokacin da ma’aikatanta suka bi ayarin yajin aiki na bai daya da shugabannin kungiyar ASUU na kasa suka ayyana kan wasu bukatu da aka gabatar a gaban gwamnati.
Gwamnatin Jihar Kaduna ce ta kafa Jami’ar Jihar Kaduna a shekarar 2004 tare da kaddamar da dokar Jihar Kaduna mai lamba 3.
Sai dai ‘ya’yan kungiyar ASUU na jami’ar sun shiga yajin aikin ne a fadin kasar domin nuna adawa da yadda ilimin jami’o’in ke kara tabarbarewa a Najeriya, musamman kalubalen rashin kudi da gwamnati ke fuskanta, da rashin jin dadin ma’aikata da dai sauransu.
Akwai sauran jami’o’in gwamnati a Najeriya da ‘yan kungiyar ASUU suka ki shiga yajin aikin da ake yi a fadin kasar. Sun hada da Jami’ar Jihar Kwara, Jami’ar Jihar Osun, Jami’ar Jihar Legas, da Jami’ar Ambrose Alli ta Jihar Edo, da dai sauransu.
Gwamna El-Rufai ya yi barazanar ne bayan sama da watanni biyar da ma’aikatan cibiyar suka shiga yajin aiki wanda ya bayyana hakasa matsayin hadin kai, inda ya yi kira gare su koma bakin aiki cikin gaggawa ko kuma a dakatar da aikinsu.
ASUU ta gabatar da kudirin dokar sanya idanu ga ‘ya’yan masu hannu da shuni da ke fita kasashen ketare karatu
Kungiyar malaman jami’o’i, ASUU, ta yi kira da a samar da kudirin doka da zai tsara yadda ‘ya’yan jami’an gwamnati ke shiga makarantun da ke ketaren Najeriya.
Shugaban Jami’ar Neja Delta reshen Wilberforce Island Farfesa Kingdom Tombra ne ya bayyana haka a wata zanga-zangar hadin kai da kungiyar kwadago ta Najeriya NLC ta shirya a ranar Talata a Yenagoa.
Kungiyar NLC ta gudanar da zanga-zangar ne a fadin kasar domin nuna goyon bayanta ga kungiyar ASUU da sauran kungiyoyin da ke da alaka da harkar a lamarin jami’o’in gwamnati a Najeriya.
“Idan aka yi haka, za a samar da ingantacciyar al’umma ta hanyar bunkasa manyan cibiyoyin ilimi da inganta kudade na tsarin jami’a a Najeriya.
“Idan aka yi haka, za a samar da ingantacciyar al’umma ta hanyar bunkasa manyan cibiyoyin ilimi da inganta kudade na tsarin jami’a a Najeriya.
“Wannan gwagwarmayar ba wai adawa da gwamnati ta ke yi ba, a’a ta bangaren ma’aikata da masu mulki ne kuma zamu jajirce akan haka sosai.
“Idan masu hannu da shuni za su je jami’a Daya da Dan talaka, ba na jin za a sake yajin aiki.
“Idan ‘ya’yansu za suyi karatu a Gida Najeriya za su nuna cikakken goyon baya ga tsarin jami’a da kuma manyan makarantun Najeriya,” in ji shi.
Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:
Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: hello@labarunhausa.com