34.9 C
Abuja
Monday, March 20, 2023

Zakaran da Allah ya nufa da chara:Bankin duniya ta nemi yarinyar da ke lissafi kamar kwamfuta

LabaraiZakaran da Allah ya nufa da chara:Bankin duniya ta nemi yarinyar da ke lissafi kamar kwamfuta
9f04d1dd4182fb93

Saratu Dan-Azumi, wata ‘yar matashiya daga jiharKano ta sake samun daman gurbin karatu saboda kwakwalwan da Allah ya bata na kwarewa a fannin Lissafi. Kwanan nan aka gano cewa yarinyar ashe ba ta zuwa makaranta amma duk da haka tana iya lissafin lambobi kamar mai aiki da kwanfuta,wanda har ta yi nssarar samun talafin karatu daga gidauniyar Bashir Ahmad, BAF.
Wani tallafin karatu ga Saratu
Har wayau ta sake samun sabon tayin gurbin karatu wanda ya fito daga Gidauniyar Ƙaddamar da Ɗaliban Mata na Ƙarfafawa (AGILE), shiri ne da Bankin Duniya ke taimako.
Jami’in Sadarwa na aikin, Aliyu Yusuf ya ce shirin zai sanya Saratu a makaranta.
Ga abinda ya ce:
A ziyarar da tawagar ta kai Masarautar Gaya, an gayyaci yarinyar da iyayenta zuwa fadar sarkin. “Wakilin ma’aikatar ilimi ta jiha da tawagar AGILE sun yi wa mai martaba sarki, Alhaji Ali Ibrahim-Abdulkadir bayani kan aniyar tallafawa karatun yarinyar.”
Na bar makaranta ne saboda cin zarafi
Saratu ta bayyana cewa ta bar makaranta a matakin firamare hudu ne saboda yadda abokan karatun ta suka zage ta, ta ce ta shirya komawa makaranta, amma ba ta shirya komawa makarantarta ta baya ba, inda ta ci zarafinta. Mates. Kalamanta, kamar yadda Premium Times ta ruwaito, ta nakalto Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya: Kaes-yarinya.

Akwai masu bin baki: Bidiyon karamar yarinya a Dubai tana yi wa su Maryam Yahaya turanci

Wani bidiyo ya yi matukar daukar hankula wanda aka ga jarumar Kannywood, Maryam Yahaya, Minal Ahmed, Momi Gombe da wata kawarsu mai suna Maryam su na ta turanci tare da wata karamar yarinya, shafin Real Ado Gwanja na Facebook ne ya ruwaito.

Da alamu sun dauki hankalin yarinyar ne wanda hakan yasa ta kasa hakuri har sai da tayi musu magana.

Kamar yadda yarinyar tace, sunanta Rumaisa inda ta bukaci su gabatar mata da kawunansu daya bayan daya.

Ta ce sun burgeta, kuma zata so sanin daga inda suke. Anan ne su ka sanar da ita cewa daga Najeriya su ke, ita kuma ta fada musu daga Pakistan take.

Ta ci gaba da jan zancen da tsawo har take cewa Najeriya a Nahiyar Afirka take koh?

Bidiyon ya yi matukar daukar hankalin mutane. Amma dai wasu suna ganin bin baki jaruman suke yi don da alamu Minal ce kadai ta iya tabuka turancin dakyau.
Tsokacin jama’a karkashin bidiyon

Ga tsokacin mutane karkashin bidiyon:

Fadila H Aliyu tace:

“Sai wow wow su ke yi.”

Saman Na Ta’ala yace:

“Mafi yawan masu kwament anan din ma ba turancin suke ji ba duk yan kano ne.”

Yahuza A Hassan yace:

“Zanso ace Musa mai sana’a na nan.”

Umar Attahir yace:

“Wasu na cin baki.”

Bin Isma yace:

“What is your name kawai Maryam yahaya ta sani! Anata zubo turanci sunyi shiru sai yake suke, Minal ce me kokarin amsawa. Su momi sai washe baki ake kamar ana shooting.”

Aliyu Muhammad Bashir yace:

“Alamu sun Nuna Maryam Yahaya da momy befi sau uku-uku su ka je prim
Abubakar Muhd Olan yace:

“Minal ce kadai ta iya yaren dakyau, sauran duk bin baki su ke yi. Lamarin ya bani dariya.”

Ku duba wasu labaran mu

Check out other tags:

Labaran da suka fi tashe