Shugaban kasar Ukraine, Volodymyr Zelenskyy, ya bukaci Najeriya, Kwaddibuwa da sauran kasashe na yankin Afirka su tallafawa kasarsa akan rikicin da ke aukuwa tsakaninta da Rasha wanda ya ki ci ya ki cinyewa, Aminiya ta ruwaito.
Kamar yadda ya bayyana, sun dade da tattaunawa da shugabannin kasashen guda biyu da wasu na yankin Afirka don ganin sun gina alaka mai kyau ta tattalin arziki.
Yayin taron manema labarai wanda su ka yi ta yanar gizo ranar Alhamis, shugaban ya ce kudaden jarin da kasarsa ta zuba a kasashen yankin Afirka za su habbaka tattalin arzikinsu tare da samar da wadataccen abinci.
Ya ci gaba da cewa:
“Mun yi waya inda mu ka tattauna da shugabannin kasar Najeriya da kwaddibuwa da wasu kasashen daban-daban. Na yarda da cewa duk da yanayin yakin da muka tsinci kanmu, ya dace ace akwai alakar cinikayya mai kyau tsakaninmu.
“Abu ne mai matukar wahala a samu daga wurinmu amma zai yi dacewa ace kasashen Afirka sun hada kai don samar wa kawunansu mafita a bangaren wadatar abinci.
“A halin da muke ci, ba za mu iya shiga kasuwannin Afirka ba kasancewar Rasha ta toshe ko ina, amma duk da haka za mu iya ganin akwai hanyoyin cinikayya wadanda za mu iya yin amfani da su.”
Yayin da aka tambaye shi lokacin da yake hasashen yakin da ke tsakaninsu da Rasha zai zo karshe, cewa ya yi har sai lokacin da duniya ta tallafa musu.
A cewarsa:
“In har Putin ya ki mubaya’a, za a yi fama da karancin abinci. Hakan kuma zai shafi gaba daya duniya. Duk da cewa ba mu muka fara kai farmaki a yakin ba, amma za mu iya kawo karshensa.
“A matsayina na shugaban Ukraine, na nemi tattaunawa a lokuta daban-daban, amma duk da haka sun yanke shawarar halaka mu bayan mamaye mu. Bai dace hakan ya ci gaba da faruwa ba. Ya kamata kashen Afirka su hada kai wurin tallafawa Ukraine.”
Kasar Saudiyya ta damke mutumin da ake zargi da taimakawa dan jaridar kasar Isra’ila shiga garin Makka
An kama wanda ake zargi da taimakawa wajen shigar da dan jarida da ba musulmi ba cikin birnin Makkah mai tsarki, wanda hakan ya sabawa dokar haramta wa wadanda ba musulmi ba shiga garin.
Ya yi amfani da ziyarar shugaban kasar Amurka ya zagaye garin Makkah
Jami’an Saudiyya sun sanar a ranar Juma’a cewa dan jaridar kasar Isra’ila Gil Tamari, wanda ya je Saudiyya don bayar da rahotannin ziyarar da shugaban Amurka Joe Biden ya kai a can, ya yi amfani da damar don shiga masarautar, ya shiga cikin birnin Makkah, ya yi zagaya tare da watsawa gidan talabijin na Channel 13.
Sakin bidiyo ya haifar da cece-ku-ce
Watsa wannan bidiyo ya haifar da cece ku ce da kuma gargadin cewa zai iya lalata shirin da ake ganin ya wanzu tsakanin Saudiyya da Isra’ila.
Dan kasar ta Saudiyya shi ne ya taimakawa dan jaridar, wanda ke da izinin zama dan a kasar Amurka, zuwa babban birnin Makkah ta hanyar da aka kebance don musulmai kawai,wanda hakan ya sabawa ka’idoji.
Dole ne a kiyaye ka’idoji
Duk masu shigowa cikin masarautar dole ne su mutunta kuma su bi ka’idoji, musamman wadanda suka shafi wurare masu tsarki.
“Duk wani cin zarafi za mu dauke shi a matsayin laifin wanda baza a amince da shi ba,” in ji jami’in ‘yan sanda.
Jami’in ya ce an kuma yi karar dan jaridar “wanda ya aikata laifin” zuwa gaban kotu.
Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayinku a wajen sharhi dake kasa.
Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:
Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: hello@labarunhausaagmail-com