27.5 C
Abuja
Thursday, March 23, 2023

Ban damu ba don yarana sun girma sun ga hotunan tsiraicina su na yawo a soshiyal midiya, Shugatiti

LabaraiBan damu ba don yarana sun girma sun ga hotunan tsiraicina su na yawo a soshiyal midiya, Shugatiti

Shugatiti, jarumar kasar Ghana kuma ma’abociya bayyana tsiraici ta ce bata damu ba don a biyata kudi ta yi fim tsirara, DklassGh.com ta ruwaito.

A wata tattaunawa da aka yi da ita a Asempa FM, ta ce bata damu da caccakar mutane ba a kafafen sada zumunta saboda yanayin ayyukanta.

Ta bayyana cewa tana jindadi idan taga masoyanta su na yabawa da bidiyoyi ko hotunanta.

Shugatiti ta kara da cewa za ta iya yin tsirara akan kudi don tana ta samun makudan kudade ta kafafen sada zumunta.

Daga baya ta kalubalanci wani ya gwada bata $30,000 ya gani idan bata yi tsirara a tattaunar kai tsaye da take yi a kafar sada zumuntar Facebook ba.

Ta kara da cewa ko nadama ba za ta yi ba don yaranta sun girma sun ga hotunan tsiraicinta su na yawo a yanar gizo.

Kamar yadda tace:

“Zan iya fim tsirara idan aka biyani $30,000 kuma ba zan yi nadama ba don yarana sun girma sun ga hotunan tsiraicina suna yawo a yanar gizo ba.”

Har ila yau ta bayyana cewa tana soyayya da wanda ‘yan uwansa su ka san aikinta. Ta kara da cewa:

“Nan gaba zan yi aure. Ina soyayya da wani wanda ‘yan uwansa sun san tarayyarmu.”

Buhari ya umarci TikTok da sauran kafafe su cire duk wata wallafar tsiraici ciki awanni 24

Gwamnatin Tarayya karkashin mulkin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta bai wa duk manyan kafafen sada zumuntar zamani kamar Instagram, Facebook, Twitter, WhatsApp da TikTok umarnin cire duk wata wallafa mai dauke da tsiraici, lalata ko kuma wani abu na rashin da’a cikin awanni 24, Instablog9ja ta ruwaito.

An samu wannan bayanin ne cikin sabbin dokokin amfani da kafafen sada zumunta ko yanar gizo da aka saki.

Kamar yadda dokar ta nuna:

“Duk wadannan kafafen na yanar gizo su yi gaggawar cire duk wasu wallafe-wallafe da ke dauke da tsiraici, lalata da sauransu wadanda aka shirya don tozarta mutane.

“Wajibi ne kafafen su dinga kula da korafi wurin sauke duk makamanciyar wallafar tsiraici cikin awanni 24.”

Dokar ta kuma bayar da umarnin a cire duk wata wallafa da ke kalubalantar wani ko kuma hukumar da ke karkashin gwamnatin tarayya.

Har ila yau gwamnati ta umarci kafafen da su tabbatar ba a sake wata wallafa makamanciyar hakan ba.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

WhatsApp Group

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: hello@labarunhausaagmail-com

Ku duba wasu labaran mu

Check out other tags:

Labaran da suka fi tashe