LabaraiDa yogot ya siye zuciyata, Zainab Yusuf, wacce ta...

Da yogot ya siye zuciyata, Zainab Yusuf, wacce ta hadu da mijinta a Twitter

-

- Advertisment -spot_img

Zainab Yusuf da Rayyan Tilde a wata tattaunawa da shafin BBC Hausa yayi da su sun bayyana yadda aka yi su ka hadu a Twitter har abin ya kai ga aure.

Zainab asali ‘yar Kano ce yayin da Rayyan Tilde dan Jihar Bauchi ne. Rayyan ya shaida cewa ya fara yi mata magana amma bata amsa mishi ba.

Daga bisani akwai wani abokinsa, Sadiq Kurfi wanda shi ma ya san ta yayi masa iso gareta bayan ya je Kano.

A bangarenta, ta ce bayan ya yi mata magana sakamakon yadda mutane ke tura mata sako yasa bata duba nashi ba balle ta amsa har sai bayan Sadiq ya mata magana.

A zuwansa na farko ya kai mata Yogot wanda hakan ya yi matukar burgeta kuma washegarin ranar ne ranar zagayowar haihuwarta inda ya kara kai mata wata kyautar.

Rayyan ya ce kasancewar karamar kyauta yayi mata amma ta shiga farin ciki kwarai, hakan ya ba shi kwarin guiwa inda ya ji ta shiga ransa.

Ita kuma a bangarenta, ta ce da yogot din da ya kawo mata ya siye zuciyarta don tana son yogot sosai.

Yayin da aka tambayeta idan bayan ya kawo mata kyautar zagoyowar ranar haihuwarta ne su ka fara soyayya, cewa Zainab tayi:

“Eh gaskiya tun farko ma da yazo din, yogot din da ya kawo min ya siye zuciyata. Kuma da yadda ya gabatar min da kansa.”

Ta bayyana cewa ta kula da wallafe-wallafensa na Twitter akan addini yake yi sannan ko gyara zai yi wa mutum cikin mutunci yake yi ba cin fuska ba.

Ga bidiyon tattaunawar tasu da BBC Hausa:

A karshe dai jaruma Mercy Aigbe ta karbi musulunci bayan aure da mijinta musulmi babu dadewa

Jaruman masana’ntar finafinai na kudancin Najeriya, sun hadu da sauran masoya jaruma Mercy Aigbe, inda suke tofa albarkacin bakin su akan rungumar addinin sabon biloniyan mijin nata da tayi, wato Kazeem Adeoti. 

Sharhin mutane akan wallafar da jaruma Mercy Aigbe din tayi

Mutane da yawa sun yi sharhi akan sakon Jarumar wanda ta wallafa a shafin ta na instagram a yanar gizo, wanda a ciki take tunkaho da sabuwar shigar da ta bayyana a ciki domin martani ga masu kushe ta. 

Kyakkyawar Jarumar wacce uwa ce ga yara biyu, ta nuna farin cikin ta da yanayin da take ciki a yanzu, da kuma matakin da take da burin shiga akan sana’ar ta a nan gaba. 

Mercy Aigbe din, ta wallafa bidiyo a karshen sati, a shafin ta na instagram wanda a ciki take nuna jin dadin shigar da tayi a matsayin ta na musulma kuma matar aure. 

Tayi alfahari da kasancewar ta mata agurin musulmi

Jarumar, wadda shigar ta ta nuna cewa lallai ita matar wani mai riko da addinin musulunci ce, tace ta dauki aniyar zama cikakkiyar Hajiya da gaske, kamar yadda kalmar take nufi. 

Tace : “Bazan yi karya ba, amma tabbas ina jin dadin wannan shiga ta Hajiya, mai yiwuwa nima zan zama Hajiya ta gaske, abin yana yi min dadi sosai, koma dai menene Allah daya muke bautawa”

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you