LabaraiWani matashi ya halaka mahaifin sa da adda saboda...

Wani matashi ya halaka mahaifin sa da adda saboda ya tada shi daga barci

-

- Advertisment -spot_img

Hukumar ‘yan sandan jihar Ogun ta bayyana cewa ta cafke wani matashi mai suna Ibrahim Sikiru, mai shekaru 27, bisa zargin halaka mahaifin sa da adda a yankin Onipanu a cikin jihar. Jaridar Pulse.ng ta rahoto

Hukumar ‘yan sanda ta yi ƙarin haske kan lamarin

Kakakin hukumar, DSP Abimbola Oyeyemi, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa ga manema labarai a Ota, inda ya bayyana cewa an cafke wanda ake zargin ne a ranar 30 ga watan Maris.

Oyeyemi yayi bayanin cewa an cafke matashin da ake zargin ne bayan wani mai suna Abiodun Sunday, ya shigar da ƙorafi a ofishin hukumar ‘yan sanda na Onipanu.

Sunday ya cigaba da bayani cewa wani maƙwabcin mamacin, wani mai gadin dare, Mumuni Ibrahim, wanda ya kawo rahoton cewa mamacin ya tambayi ɗan na sa dalilin da yasa ya ke barci bayan ya dawo ya same shi a gida daga wurin aiki.

Matashin ya fusata saboda an tayar da shi daga barci

Bayan samun rahoton, DPO ɗin Onipanu, CSP Bamidele Job, ya tura jami’an sa zuwa wurin da lamarin ya auku inda aka cafke wanda ake zargin sannan aka miƙa mahaifin zuwa babban asibiti domin duba lafiyar sa.

Ya ƙara da cewa, lokacin da mahaifin ya tambayi ɗan nasa dalilin yin barci a wannan lokaci, yaron ya fusata inda ya ɗauko adda ya sassari mahaifin na sa a wurare biyar.

Bayan samun rahoton, DPO ɗin Onipanu, CSP Bamidele Job, ya tura jami’an sa zuwa wurin da lamarin ya auku inda aka cafke wanda ake zargin sannan aka miƙa mahaifin zuwa babban asibiti domin duba lafiyar sa.

Wanda ake zargin, wanda ake kyautata zaton cewa ɗan daba ne, bai bayar da wani gamsashshen dalilin aikata wannan laifin ba a yayin gudanar da bincike.

A ranar 31 ga watan Maris, mahaifin ya rasu yayin da yake amsar magani a asibitin, inda ‘yan’uwansa su ka haƙiƙance kan binne sa kamar yadda addinin sa ya tanada. A cewar sa

A cewar sa

Matashi ya rotse kan mahaifinshi da tabarya ya mutu har lahira a jihar Yobe

A jiya Laraba 9 ga watan Fabrairu 2022, Rundunar ‘yan sandan jihar Yobe, ta ruwaito cewa wani matashi dan shekara 20, mai suna Mai Goni, ya kashe mahaifinshi, Goni Kawu da tabarya a Masaba, cikin karamar hukumar Bursari.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Dungus Abdulkarim, shine ya sanarwa da Kamfanin Dillancin Laabarai na Najeriya (NAN), cewar lamarin ya faru ranar Talata da misalin karfe 7:30pm na dare.

Shin kuna da wani abin cewa? za ku iya bayyana ra’ayoyin ku a wajen sharhi dake kasa.

Ku cigaba da kasancewa da jaridar mu domin cigaba da samun sahihan labarai kai tsaye a wayoyinku, za kuma ku iya biyo mu a shafukanmu na sadarwar kamar haka:

Facebook Page

Twitter Page

Telegram Channel

Ko kuma ku aiko mana da sako ko sharhi ta adireshin mu na Email kai tsaye: info@labarunhausa.com

Sharif Lawal
Sharif Lawal
A graduate of Botany from Ahmadu Bello University Zaria, Who hailed from Dabai in Katsina State

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Latest news

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su ka lamushe wiwi mai nauyin 200kg bayan sun kwace ta...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama shi sannan a sakaya shi saboda ya lakada mata na...

Wata mata ta haihu a masallacin Annabi

Wata mata cikin masu gudanar da umra ta haihu a masallacin ma'aiki dake Madinah wacce ta samu taimakon wasu...

‘Yan gida daya su 11 sun mutu bayan cin wani abinci

Aƙalla mutane 11 ne 'yan gida ɗaya aka tabbatar da sun mutu bayan cin wani abinci da ake zargin...
- Advertisement -spot_imgspot_img

Matashi ya kaɗu bayan gano cewa budurwar sa a kango take rayuwa

Wata matashi ɗan Najeriya ya shiga kaɗuwa matuƙa bayan gano cewa budurwarsa ta tsawon wata takwas a cikin wani...

An zaɓi mace musulma ‘yar majalissar jiha a Amurka

Nabeela Syed, 'yar asalin ƙasar Indiya ta kasance mace musulma ta farko da aka zaɓa a matsayin 'yar majalissar...

Must read

Ɓeraye ne su ka bushe wiwin da mu ka ƙwace mai nauyin 200kg, ‘Yan sanda

‘Yan sandan Indiya sun koka kan yadda beraye su...

Daɗi miji: Bayan an kulle shi saboda ya laƙada mata duka, matar ta yi belin mijinta

Wata mata ta yi belin mijinta bayan an kama...
- Advertisement -spot_imgspot_img

You might also likeRELATED
Recommended to you